Showing posts with label Nigeria. Show all posts
Showing posts with label Nigeria. Show all posts

Sunday 9 February 2020

Yadda ake Scoope potato

Yadda ake Scoope potato

Scooped potato🍟🍟



🍸🍸🍸🍸🍸🍸🍸🍸

🍟large boiled or friedpotato cut in half cooked meat🍟 😋

🍟onions
🍟seasoning
🍟oil
🍟pepper
🍟egg

🍸🍸🍸🍸🍸🍸🍸🍸
🍟procedure
In oil over the pan
add onions, meat, pepper, prefered  seasoning and veges( you can add eggs if you like) when ready set aside...  get potato's and scoop the middle out ... Put the meat inside and enjoy😋
YADDA AKE COCONUT PANCAKE

YADDA AKE COCONUT PANCAKE

COCONUT PANCAKE 🍜🍜🍜🍷🍷🍷
 

                         
 INGREDIENT,   
  flour
sugar
Pinch of salt
baking powder
Milk
Egg
teaspoon of oil
coconut                  method da farko zakiyi mixing din ingredients naki gaba daya a bowl Sai ki sa ruwa kiyi mixing dinsu mai kyau Amma Kar yayi ruwa ruwa Dan Kar ya Sha mai daman already kin goga coconut dinki Sai ki zuba a ciki da coconut flavor dinki Sai ki sake mixing nasu mai kyau ki soya Kamar soya Kwai.
YADDA AKE FRIED SPAGHETTI

YADDA AKE FRIED SPAGHETTI

🍜FRIED SPAGHETTI


INGREDIENTS
spaghetti
Meat
Carrot
Green beans

Pepper
Onion
Tomatoes
Garlic
Ginger
Method da farko zakiyi per boiling spaghetti dinki da gishiri da dan Mai in yayi Sai ki wanke ki ajiye a gefe, Sai ki soya su kayan miyan da garlic nd ginger ki Daman already kin Riga da kin yayyanka su carrot dinki into shape da kike so Sai ki zuba su Akan kayan miyan suma Sudan soyu Sai kisa ruwa kadan kisa naman ki dakika tapasa, Maggi, curry, thyme da duk spices da kike so Sai ki zuba spaghetti ki akai, in kina so Zaki iya yanka wani albasa ki kara akai da attarugu Dan ya bada Kala da kamshi Sai ki rufe in yayi Sai ki sauke acida coleslaw, Aci dadi lfy
YADDA AKE SULTAN CHIPS

YADDA AKE SULTAN CHIPS

🍜🍷SULTAN CHIPS 🍜



  INGREDIENT
potatoes
Egg
Carrot
Green pepper
Onion
Green beans
Garlic nd ginger
Pepper
Method da farko zaki yanka potatoes dinki into kowane shape Sai ki soya Sama Sama Sai ki ajiye a gefe ki soya su kayan miyanki daman already kin yanka su carrot naki a tsassaye Sai ki zuba su Akan kayan miyan naki Amma banda Kwai in suka soyu Sai ki kada egg naki ki zuba a Kai Sai ki rage wuta inyayi Sai ki diga ruwa kadan akwai kisa potatoes Sai ki gaurayawa mai kyau Sai ki Bari yayi Kamar 5mins Sai ki sauke,
YADDA AKE COCONUT  CUSTARD

YADDA AKE COCONUT CUSTARD

COCONUT  CUSTARD

=method da farko za kiyi blending din coconut dinki Bayan kin Gama Sai ki tace ruwan ki dama custard dinki da shi Sai ki zuba tapasassen ruwan akai Kamar Dai Yadda ake dama koko Bayan kin Gama kisa sugar, flavor nd milk. Idan kina so Zaki iya goga coconut din Sai ki zuba akai Bayan kin Gama Kenan.
YADDA AKEYIN Black & White Glazed Donuts

YADDA AKEYIN Black & White Glazed Donuts

Black & White Glazed Donuts



Ingredients

Donuts:
1 cup flour
1 tsp baking powder
½ tsp baking soda
⅛ tsp salt
⅔ cup white granulated sugar
1 egg
½ cup buttermilk
2 Tbsp melted butter
2 tsp vanilla
1 oz baking chocolate, melted
2 Tbsp cocoa powder
1 Tbsp buttermilk
Icing:
1 cup powder sugar
3 Tbsp heavy cream
1 tsp vanilla
Chocolate Icing:
¾ cup powder sugar
2 Tbsp cocoa powder
4 Tbsp heavy cream

Instructions

Preheat
oven to 350 and grease a donut pan.In a large mixing bowl, whisk egg, sugar, buttermilk, melted butter and vanilla together until smooth.Sift in all dry ingredients and whisk until all incorporated.Take out half the batter and pour it into a piping bag. Set aside.Whisk in cocoa powder, melted chocolate and 1 Tbsp buttermilk into remaining batter. Whisk until smooth. Pour chocolate batter into another piping bag.Cut the tips off both piping bags, leaving only about ½ inch opening.Squeeze batter into the donut cups of the pan, using both bags at the same time (one in each hand), in the half-circle motion, making sure that half the donut is chocolate and the other half vanilla. Make sure there is an even amount of batter all around.Bake for 10-11 minutes and let donuts cool on the wire rack, just until the donuts cooled enough to be handled.Spread paper towel under the cooling rack to catch icing drippings.While donuts are cooling, prepare the icing.Heat up all heavy cream and vanilla until hot but not boiling. Combine cocoa powder and ¾ cup powder sugar in one bowl and place 1 cup of powder sugar in another bowl. Whisk in 4 Tbsp of hot heavy cream into chocolate mixture until all smooth. Whisk in 3 Tbsp of hot heavy cream into powder sugar in another bowl until all smooth.You can either carefully dip top halves of donuts into icing or you can pour each icing over the donut halves with a spoon. I found it much easier to pour some icing over the donuts.Let donuts sit for 5-10 minutes and enjoy.

Saturday 8 February 2020

YADDA AKE ROSTED TILAPIA FISH

YADDA AKE ROSTED TILAPIA FISH

ROSTED TILAPIA FISH 



          METHOD                                        Da farko idan kin wanke kifinki ki Mai kyau Sai ki Nemi kwana kisa olive oil Kamar 2 table spoon haka Sai ki sa miggin ki,go kisa yajin ki, kisa dakekken attarugu, ki yanka albasa aciki, ki daka garlic kisa a ciki Sai ki matse lemon tsami guda daya akai Sai ki gauraya su Mai kyau Sai ki nema kitchen towel ki goge kifin Dan Kar yayi ruwa ruwa inkin goge Sai ki shafa duk wannan hadin akai daman already kin kunna oven naki Sai kisa a farantin gashin ki gasa Sai kina kula dashi Kar ya kone kina juyawa duk juyawan da kikayi Sai ki shafa hadin ko akai Dan ya shiga jikin kifin in ya gasu Sai ki sauke.                            Sai Kuma source da Zaki sa akai ki jajjaga kayan Miyan Sai ki soya Sai kiyi slicing din albasa da green pepper kisa akai da Dai duk abunda kike so kiyi garnishing din shi da shi
ABUNDA KE BOY'E

ABUNDA KE BOY'E

[7:21PM, 11/21/2017] 💧💧 Feedohm💞: 💧
💧 *ABUNDA KE BOY'E……*
       《Almost True Life Story》
             
                   🍁🍁
                      💧


© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


       *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*


*DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JINK'AI……*

*SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《UMMANA》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
  *GA DUKKAN MASU SUNA HAFSAT DAKE FADIN DUNIYAR NAN……*

 *UMMANA ALLAH YA JIBANCI LAMURRANKI ALLAH YA HASKAKA RAYUWARKI TA DUNIYA DA LAHIRA……🙏🏻*




*1 & 2*



  "Ayyiriri yiriri!Buwale!Asibi!Baraka!Lanto!Kande!kai dukkan Jama'an garin ga ku fito ku gane mani sabon lamari a gidan MALAN LADO………"Cewar wata yar tsamurmurae tsohuwa da ta fito kofae gidan da daurin kirji a jikinta……

  Kamar ana angazo mata da kananan yara daga gidanjen su !haka sukayi dandazo gabanta ko wace sae wurga ido take tana jiran taji me zata fadi Wasu da daurin kirji wasu ma ko dankwali bassu dashi……

 "Kundum lahiya kika tara mutane haka?ko dae tsohun Haukanne ya motsa……"Cewar wata yamutsatstsar tsohuwa da ta iso lokacin dauke da bahon Tafasa a kanta……

  Kundum ta sake rafka guda tana fadin "Yau de Hafsatu ta haihu!Mai tafasa an samu dad'in jika Sae dae mu bamu san waye Uban yaron ba……"ta karashe maganar tare da kecewa da dariyar mugunta har da rike cike……

  Sauran matan dake tsaye suka dauki wani bahaggon salati tare da taba hannunawa suna kiran "Hafsatu kam an cuci Malan lado……"

 Maitafasa kam aje bahon tafasar tayi tana fadin "Watsatstsan Zance kundum!Dama wagga rana nake jira ranar da hafsatu zata haihu wallahi sae ta bar gidan Lado……"



Shiga tayi gidan tana fadin "Ke Hafsatu fito nan munafuka dama yau nake jira sae kin fada man cikin uban waye kika haife a gidan d'ana……"

 Matan garin suka mara mata baya har cikin gidan tare da yaransu ……wasu har bisa katanga ……

  Hafsatu dake duke tsakar dakinta ……ta janyo wuka ta langa langa ta yanke cibiya da kyar sannan ta janyo wani yamutstsan tsumma ta goge jaririyar tare da nadeta cika sannan ta janyo wani tsumma ta shinfida saman lomatsatstsar katifar dake tsakar dakin ta kwantar da jaririyar……

  Jin Mai tafasa na kiranta yasa ta gabanta ya fadi ta mike idonta cike da kwallah ta fita ta tsaya bakin kofar dakin tana sadda kai kasa……

  Gabanta maitafasa tayi birki tana watsa hannu baya "Da kwarankwatsa kinci amana Hafsatu!kin ci amanar lado da aurenki kije kiyi cikin shege sannan ki haife a gidan mijinki……Ke Hafsatu kwarankwatsa da kudi gareni da kotu na makaki a birni a kasheki kowa ya huta da wannan abun kunyar……Fadan Cikin uban waye kika haifa ……?

  Cikin kuka Hafsatu tace "Wallahi inna Cikin lado ne kuma d'iyar lado ce na haifa……!

  "Lado!badae ladon mai tafasa ba……"Matan garin suka dauka tare surutai kasa kasa……

  Maitafasa kam watsa bakaken hannunta tayi saman fuskar Hafsatu tana fadin "Ubanki!Uban lado!nace Uban ladon!D'ana zaki wa sharrin Hafsatu?Ladon dake kwance tsawon Shekaru takwas kamar gawa sae yarda akayi dashi shine zaki haihu ki lik'a mashi ruwan sharri don kinga baya iya magana ……to Uwarsa Maitafasa nanan kuma ban karba ba……"

  Yar matashiyar yarinya ta shigo rike da kwaryar nono ganin gidan a cike ga maitafasa tana ta bala'i yasa ta bata fuska ta matsa tana fadin "Maitafasa lafiya aka cika mana gida haka……?

  "Ina fa lafiya Uwarki ta janyo mana abun kunya……"cewar mai tafasar tare da matsawa kusa da wata bukka tana fadin "Lado!kana ina……?

  Yarinyar ta sake bata fuska tana fadin "Shine dan rashin mutunci zaa cika mana gida haka ……inace uwar tawa tana da miji ……"

  Kundum tace "Da mijinta amma munsan ba cikinshi bane……"

  A Fusace tace "Zanci mutunciki kumdum!ku kuma ku jira har in shiga daki na fito wallahi sae,na fasawa duk shegen da na gani kai……"

  "Wa yace tayi abun kunyar……"Cewar wata mata dake tsaye bakin katanga

 Bata ce masu komae ba ta shige dakin ……ganin jaririyar tana kuka yasa ta dauketa tana jijjigawa ……

Maitafasa kam tana shiga bukkar lado ta rushe da kuka tana fadin "Lado Hafsatu ta cucemu !An cucemu lado anci amanarmu ……wallahi yai Sai na saki Hafsatu lado……"

  Kuka yake mara sauti yana kokarin daga mata hannu amma ya kasa……ido yake rufewa yana budewa da karfi hawaye na fita kamar an bude famfo ……
  "Nace kayi hakuri lado ……Dan cuta an cuceka kamarka a garinnan ace matarka taci amanarka ,to wallahi sae ta bar mana gida yau dinnan ……"

  Zata fita ya zabura ya kife tare da sakin kukan da muryar bata fita ……
Juyowa tayi tana fadin "Ka bar kukan lado nasan yarda kake ji amma,in dae ina raye lado baran,bari a ci mutuncinka ba ……"

  Fita tayi ta iske Har lokacin Hafsatun na tsaye inda ta barta tana kuka……
Kundum tace "Dan cuta an cuceku Maitafasa kamar lado a garinnan don anga baya lafiya sae a ci mutuncinsa……?

  A Fusace maitafasar ta juyo tana fadin "Ke Kundum bansan munafunci……"ta karashe maganar tana watsa hannu gaba

  Matan gidan suka dauki dariya tare da sowa ……Maitafasa kam ture Hafsatu gefe tayi ta fada dakin tana fadin "Yau zaki,bar gidannan,wallahi ……ni maitafasa uwar lado na saki Hafsatu saki uku!ke kwarankwatsa da ana saki Hamsin da yau shi na maki Hafsatu……"ta karashe maganar tana wullo jikkunan,bakon dake tsakar dakin ……

 Yarinyar dake rike da jaririyar ta mike tana fadin "Wane irin wulakancine haka wae……Wannan,rashin adalcine Ummana tana da mijinta amma dan ta haihu shine zaa mana haka?

  Rike haba maitafasa tayi tana fadin "Owo Lauratu rashin kunya zaki man ,To kema wallahi sae kin bar gidan !Uban wa ya sani ko kema ba diyar tashi,bace……"

  Ta karashe maganar tare da turota waje ……Zatayi magana Hafsatun ta rufe mata baki sannan,taja hannunta suka fita daga gidan ba tare da sun dauki komae ba ……

  Mai tafasa ta bisu tana fadin "Shegu gayyar tsiya……"

  Yayin da matan garin da kananan yara suka bisu da ihu da jefa har suka bar garin ……



# *FEEDOHM💞*
[5:44AM, 11/22/2017] 💧💧 Feedohm💞: 💧💧 *ABUNDA KE BOY'E……*
        《Almost True Life Story》

                   🍁🍁
                      💧

© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


        *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*
          *_&_*
 *_PRECIOUS HAJJA CE👈_*


*SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《Ummana》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
 *Da dukkan masu suna HAFSAT dake duniyarmu*



*3 & 4*


  K'ira'ar Shiekh Ahmed sulaiman ke tashi cikin katon falon dake dauke da mayan kujeru……Gefe daya Wani kyakykyawan matashin yarone ke bin karatun cikin natsuwa idonshi a lumshe ……
Kujeran dake kallon tashi wata yar dattijuwar mata ce itama kyakykyawa zubin larabawa ……Kallo daya zaka mata ka gano tsantsar kamar da take da saurayin ……Sannan cikin second biyu zaka gane hutu da jin dadi sun ratsa mutanen dake zaune a falon ……

  Wayarshi kirar Iphone 8 ta dauki addu'ar Shiekh sudais a hankali ta yarda bara ta dami wanda ke kusa da ita ba ……
Lumsassun idanunshi ya bude ya kalli wayar sannan ya mayar dasu ya rufe……

      "Ma'aruf ba wayarka bace ke ringing……"Kamilallar matar dake zaune ta fada tare da kurawa wayar ido……

  Bude idonshi yayi  tare da bata fuska yana fadin "Message ne ya shigo Madre……"

  Mika hannu tayi tana fadin ……"Bani wayar na gani……"

  Kamar karamin yaro yace "Madre office ne fa ake kirana……!

  Harara ta sakar mashi tana fadin "Sae ka dauka kaji me zasu fada !kuma wallahi ta tsinke sae ka kira sh……Wae me yasa kake hakane Ma'aruf? idan bara kayi aikin ba ka aje mana  ka huta ko an maka dole……?

  Kallonta yayi da lumsassun idanuwanshi yana fadin "Madre shikenan mutun bara ya huta ba kullun aiki kamar engine……"

 Banza ta mashi ta juyar da kai gefe guda……
Wayar ya bi da harara sannan yasa hannu ya dauka yayi shiru ……

   Daga dayan bangaren akace "Sir akwae wani case na AFP da akayi reporting a jihar katsina ……So yanzu aka turo kai zakayi verifying dinshi daga England……"

 Kallon Madre din yayi yaga shi take kallo "Hello……"ya fada kamar zaiyi kuka tare da yanke wayar ……
  "Madre bana jin abunda suke fada ……"ya fada kamar ya fasa ihu

  Wayarta kirar IPhone7 ta mika mashi tana fadin "Ka kirasu anan !wallahi Ma'aruf duk abunka sae ka dauki wayarsu……"

  "Madre ……!ya fada kamar yayi kuka sannan ya dauki wayar tashi ya sake kira ……
  Bai amsa sallamar da akayi ba yace "Ka turo man Number State consultant dinsu……"daga haka ya mike ya bar falon ……

  Kyakykyawar matashiyar yarinya ta shigo sanye da atampha mai ruwan goro sae zanen ganye da akawa ado da ruwan toka kayan sun dace da jikinta……
Da fara'a ta isa gurin tana fadin "Madre Barka da safiya……"

 "Yauwa Sumayya!shiga dakina saman mirrow ki dauko trcts ki kaima Ma'aruf idan ya fita ya mikawa Abbansa office ni zan fita……"

  "To……" ta amsa tare da mikewa ta shiga dakin ta dauko sannan ta fita daga falon……
Sai da ta wuce balcony sannan tayi tafiya mai tsawo ta isa wani katon part dake zagaye da glasses……Wani red abu tayi clicking a jikin kofar sannan ta bude ta shiga ……
Katon falone kamae wanda ta baro sae dae wannan ya banbanta da wacen saboda complete kayan dake falon red ne harta plasma dake ciki ……

  "Yaya Ma'aruf ……"ta fada tana bin falon da kallo……
  Banza ya mata yana zaune bisa kujeran dake bayanta ……ganin zata shige bedroom dinshi ya sashi fadin "Sumayya……"Kasan makoshi ……

 Juyowa tayi tana turo baki tare da fadin "Shine ka shareni……?
 Ba tare da ya kalleta ba yace "Menene?

Kujeran dake kusa dashi ta zauna tana fadin "Madre tace na kawo maka ka kaiwa Abba idan ka fita……"

  "Aje ki tafi……"ya fada ahankali ba tare da ya kalleta ba ……

 Ta san hanlinshi sarai ta mike a sanyaye ta bar dakin ……

《》《》《》《》

  Tafiya sukayi mai tsanin nisa sannan Hafsatun ta zube bakin wani iccen kanya tana haki ……

  "Sannu Umma……"Lauratu ta fada tana dafa bayanta ……
 A Wahale ta gyada mata kai sannan ta sa hannu ta karbi jaririyar dake ta mutsu mutsu a hannu Lauratu ……

 Mama ta bata yarinyar ta karba da sauri tana wuntsila kafafuwa ……Murmushi Lauratu tayi ta kama kafar yarinyar tana fadin "Ummana da gaske wannan diyar Baffa ce……?

 Da Sauri Hafsatun ta kalleta da idanunta da suka cika da kwalla sannan ta sadda kai tana goge hawayen ba tare da tace komae ba ……
  Jikin Lauratun yayi sanyi tare da nadamar tambayar da tawa Umman tata duk da itama tana mamakin ta yarda zaa ce umman ta haihu ……Bayan tana sane da Baffanta da yayi shekara takwas a kwance ko hannu baya iya dagawa ,a inda yake nan yake kashi yayi fitsari sae dae Umman tata ke wanke mashi ……amma rana tsaka ace Umman ta haihu dole kanka ya daure……

  "Kiyi Hakuri Umma dan Allah bansan tambayar zata maki ciwo ba ……"Lauratu ta fada tare da dafa Umma……

 Bata ce mata komae ba sae bin kafafuwanta da kallo da tayi ,wanda suke wanke da jini ……rumtse ido tayi jin wani abu na tsira a kasanta sannan ta mikawa Lauratun Yarinyar ta mike da kyar tana fadin "Mu tafi Lauratu……"

  Cire zaninta tayi ta goya diya dashi sannan ta kama hannun Umman tata suka yanki daji ……

  Wannan karan tafiya kadan sukayi suka fara hango rukuni rukunim gidajen fulani dake cikin dajin ……

  Wani Gidan gandu suka nufa ……
Yara dake wasa kusa da gidan suka dauki ihu "Ga Hasfuwalle ga hafsuwalle……"

  Matan gidan da tsofaffi suka fiffito bakin kofar gidan suna fadin "Aradun Allah da gaske Hafsuwalle ce ……Sannu Hafsuwalle ansha hanya……Harda Lauratu yasin……"

  "Ato Meye haka nake gani bayanki lauratu……?Cewar wata tsohuwa dake kama da Hafsatu kamar an tsaga kara……

  Kallon Ummanta tayi da sauri sannan ta kalli tsohuwar tana fadin "Jaririyace Inno……"

  "Ina kuka sameta……?cewar matan dake gurin kamar hadin baki ……

  Wannan karan ma sae da ta kalli Umman tata wadda ta sadda kai kasa tana hawaye sannan tace "Ta Umma na ce……"




*#HAJJA CE👈*
*#FEEDOHM💞*
[2:11AM, 11/23/2017] 💧💧 Feedohm💞: 💧💧 *ABUNDA KE BOY'E……*
        《Almost True Life Story》

                   🍁🍁
                      💧

© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


        *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*
&
*_K.A.S.Precious HAJJA CE_*👈


       *SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《Ummana》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
 *Da dukkan masu suna HAFSAT dake duniyarmu*



       Page *5-6*

    *M*uryar inno ce ta kuma dukan dodan kunnan Hafsatuwalle "wai hafsatu sai kuka kike mana daga tambaya. Shin a ina kika samu jaririya d'anya sharaf?"

Kasa d'agowa tayi ta kallesu ganin gaba d'aya idanuwan su na kanta yara da manya karaf idanuwan jummai ya sauka akan kafar Hafsatuwa da jini ke bin ta tace.

"Shiiii kenan wallahi 'yar tace ga alamar jinin haihuwa nan mun shiga uku." Gaba ki d'aya mutanan wajan suka saki salati suna tafa hannaye, hakan ya k'ara tayarwa da Hafsatu hankali cikin sauri lauratu ta ja hannun Umman nata suka doshi cikin gidan da matan suka fito.

Cikin d'akin Inno suka shiga, itama da sauri ta bisu ciki "bafa zaku zauna min a d'aki ba alhalin bansan a ina kuka samo wannan jaririyar ba."

Inno ta fad'a tana nuna jaririyar dake rungume a jikin lauratu wadda ke ta faman bacci hankalinta kwance.

A hankali muryarta na rawa hawaye sun kasa tsayawa a fuskar ta Umma tace, "jaririyata ce inno ni na haifeta yau d'innan..."

Salati Inno ta kuma saki tana kama ha6ar ta "Hafsatu tayaya kika samu cikin har kika haifi yarinya duk bamu sani ba, kuma ai munsan malam lado ba lafiya gare shi baya iya komai sai anyi mai taya kika samu ciki kuma 'yar waye..?"


*{{   }}*

   "Bari ni kundum wallahi yarinyar nan ta bani mamaki ta rasa cikin wa za tace sai lado, ladon da kowa ya sani ba lahiya ce dashi ba amma tace cikin shine..."

Mai-tafasa tayi maganar tana sosa wuyanta alamar taji kaikayi a gurin. Kundum ta sake rafka gud'a ayyirrrr-yirrrrr, "koma dai menene *Abunda ke b'oye* ya fito fili sauran bayani dai yana wajan Hafsatuwalle."

"Tallahi kinji na rantse ko kundum? Yau da ace lado lajiyar shi lau hukuncin da zai yi kan Hafsatuwalle sai ya ninka wanda na mata..."

Lado dake kwance a d'aki sai faman k'ok'arin son yin magana yake amma ya kasa, hawaye ne suka fara zubo mai masu zafin gaske. Mai-tafasa ce ta lek'a d'akin ta ganshi sai kuka yake tayi saurin k'arasawa kusa dashi cikin takaici tace...,

"Yi shiru lado nasan Hafsatu ta cuceka, ganin baka iya komai yasa ta danganta cikin nan da cewar naka ne. Kayi hakuri lado wallahi da raina da lahiya ta bazan bari a cuce ka ba.."

Lado kam banda girgiza mata kai da yake yi babu wani abunda yake, hakan shine kawai sign d'in da yake iya yi hakan yasa ko fitsari yaji baya iya fad'a sai dai ya sake shi a wando. "Kayi shiru lado dan babu wanda ya yadda da zance Hafsat..."

Mai-tafasa ta fad'a tana fita daga d'akin ta karasa gurin kundum dake tayawta surfan masara suka ci gaba da tattaunawa akan maganar....,


*{{  }}*

     Bayan fitar Sumayya da kyar Mu'aruf ya mik'e, bathroom ya shiga wanda ya had'u yaji komai ya k'arasa ya shiga jarkuse wanda aka cika da ruwa mai k'amshi. Ya dad'e a ciki kafin ya fito da bathrobe a jikin shi. Dressing room ya wuce wanda shima ya gaji da tsaruwa sosai, direct underwears drawer ya wuce ya bud'e gasu nan ajere kamar a company ya zari vest da trunks yasa saka sannan ya k'arasa dressing mirror ya zauna kan stool yana shafa lotion mai kamshi tamkar bayasan shafar.

Drawern kayan shi ya k'arasa ya bud'e wadda baki d'ayan gurin suit's ne kamar na siyarwa kala-kala ya d'auki black color d'in ya sanya bayan yasa ta cikin white color...,

Gashin kanshi ya gyara sannan ya bi duk ilahirin jijin shi da turaruka kusan kala 6 masu kamshi ya sanya socks da sandal ya fito daga room d'in, be koma side d'in Madre ba kawai ya wuce parking lot ya bud'e motan shi white paradox dake ta kyalli ya bud'e yashi ga, office d'in abban shi ya fara zuwa...







*_HAJJA CE_*👈
&
*_FEEDOHM_*💞
[2:40AM, 11/23/2017] 💧💧 Feedohm💞: 💧💧 *ABUNDA KE BOY'E……*
        《Almost True Life Story》

                   🍁🍁
                      💧

© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


        *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*
     *&*
*_K.A.S Precious HAJJA CE👈_*


*SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《Ummana》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
 *Da dukkan masu suna HAFSAT dake duniyarmu*


     Page *7-8*


*Y*ana shiga office din ya iske Abban nashi baya ciki Messenger Office din ya tambaya ina Abban ?yace mashi sun shiga meeting ne ……Sakon ya bashi ya juya ya fita tare da gaisawa da wadanda ke mashi magana ……

WHO Office dinsu ya nufa ,Tunda ga waje zaka fahimci wayeshi ta yarda dukka mutanen gurin suke bashi girma Cikin mutunci yake amsa masu  gaisuwarsu saboda babu wanda bai girmeshi ba a gurin kawae Sa'ar Rayuwa Allah ya bashi……
Hadadden office dinshi ya nufa wanda ke dauke da kayan alatu na rayuwa
Coat dinshi ya cire sannan ya ja kujera ya zauna Bude laptop din dake saman table din yayi tare da saka siririn glass din dake aje kusa da wasu tarin files……Cikin natsuwa ya fara bincike yanayi yana lumshe idonsa wanda ya rigaya ya zame masa d'abi'a……
Duk wani abunda ya shafi case din da garin da abun ya faru an rigaya an turo mashi ta email dinshi har ta hotel da room number da zai sauka an turo mashi da number State Consultant da LGA facilitator dinsu ……

Dogon tsaki ya sake lokacin da ya rufe laptop yana fadin "Gwadabniya" tare da tabe baki……Bai bata jin sunan garin ba a rayuwarshi bare ya saka ran zaije wata rana ……Kara sakin karamin tsoki yayi ya dafe kanshi kamar ya sake ihu tare da cire glass din……

Komawa yayi bisa tarin takardun da ke aje ya fara bincikawa cikin natsuwa har ya fitar da da wani file。 sannan ya mike ya fita ya baiwa Messenger dinshi yace ya kaiwa Doctor Habib…………Gida ya nufa don ya shiryawa tafiyar saboda yarda ya tsara bara yayi kwana biyu ba a garin……


《》《》《》


 *M*alam Sani Mahaifin Hafsatu yayi sallama gidan…… tun kafin ya karaso cikin gidan Jummai ta tare shi a zaure tana rike da tabarya "Malan Hafsuwalle ta zo……" ta fada murya kasa kasa ……

  "Ahhaba ki ce baki mukayi yau, Marhaban da mutanen Keteriya!amma ita haka ake zuwa babu sanarwa ……?ya karashe maganar yana kokarin zagayeta ya shiga cikin gidan

 Cikin sauri tace "Har da jaririyar ta danya shar Malan……"

Yar dariya yayi irin ta manya sannan yace "Ai kunga abunda yafi haka indae Hafsatuta ce ,akwae janye janye yanzu haka ta makwabtace ta dauko!Hafsatu a akwae son mutane……"

  Murya kasa kasa tace "Kai Malan Hafsatun ka ta haifeta da cikinta…"ta karashe maganar tana nuna cikinta da hannu

  Wani kallo ya jefa mata yana fadin "Bana son zancen banza jummai,Malan lado ya warkene?

  Watsa hannu baya tayi tana fadin "Ina fa ya warke malan?abun kunyane ta janyo maka da mutuncinka a garin nan……"

  Bai ce mata komae ba ya wuce ya shiga gidan yana kwalawa hafsatun kira,Daga jin yarda yake kiran kasan bana kwanciyar hankali ba ne ,Dukka mutanen dake cikin d'akunansu suka fito sukayi cirko cirko suna maganganu kasa kasa wanda daga ji kasan gulma suke……Daga Hafsatun har Inno da lauratu suka fito waje……Hannu Hafsatun ya kurawa ido sannan ya kalli fuskarta ……

  Jikinshi yayi sanyi lokaci guda ya kalleta yana fadin "Hafsatu ina kika samo jaririya haka…?

  Kasa magana tayi sae kukan da ta saki a hankali tana kallon kasa ……
  "Dake nake Hafsatu!ina kika samo jaririya danya haka……"

  "Jaririya ta ce Ard'o…" ta fada cikin kuka…

 "Mijinki ya warkene Hafsatu……?ya tambaya cikin sanyin jiki

 Girgiza kai tayi tana share hawayenta ……
  "To Ina kika samota Hafsatu? d'iyar wacece haka?
  "Ard'o d'iyar Lado ce……!ta fada har lokacin tana kuka

  "Watsatstsan Zance Hafsatu ……Wanga zancen naki ko Shanun gidannan bara su karb'a " Cewar mutanen gidan kamar hadin baki……

   Da Sauri ya karbi jaririyar daga hannunta ya nufi wata katuwar bukka yana kwalawa Sallau kira …Sallau ya fito daga bayan gida rike da katuwar sanda a hannunshi yana fadin "Shanun ne suka balle Ard'o"

  "Fiton da Turmin kurtumi Sallau……"Cewar Ard'o yana nuna bukkar da hannu……

  Matan gidan suka dauki magana kasa kasa tare da kallon juna suna taba hannuwa……

   "Malan karka yi kisan kai ,ka dae san wannan jaririyar bata halak ba ce tunda tsawon shekaru takwas mijinta baya da maraba da gawa……"Cewar Jummai tana kokarin karbar yarinya

  Cikin matan wata tayi zagal tace "A Kara ya kasheta da wannan mugun abun kunyar da ake niyyar dauko mana"

 Hafsatu banda kuka babu abunda takeyi ,ita kam lauratu shiru tayi tana kallon ikon Allah ,haka Inno bata iya cewa komae ba don ta yarda da Hafsatu bara ta aikata abu mai muni irin haka ba ……

 Gangaro da katon bak'in Turmin ne yasa gidan ya kara kaurewa da maganganu kasa kasa……

Ard'o bai ce komae ba ya jefa yarinyar cikin Turmin ya ma sallau alamar da ya miko mashi tabarya……

  Babu musu Sallau ya mika mashi katuwar tabaryar tare da ja baya……



*HAJJA CE👈*
*FEEDOHM💞*
[3:57PM, 11/24/2017] 💧💧 Feedohm💞: 💧💧 *ABUNDA KE BOY'E……*
        《Almost True Life Story》

                   🍁🍁
                      💧

© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


        *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*
&
*_K.A.S Precious HAJJA CE*👈


*SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《Ummana》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
 *Da dukkan masu suna HAFSAT dake duniyar mu*



        Page *9-10*


    *G*aba ki d'ayan mutanen gurin jikin su yayi sanyi dan sunsan yau kwanan jaririyar ya kare. 6angaran Hafsatuwalle kuwa ko d'ar bata jiba sai dai hankalinta a tashe yake dan tasan ko anyi wannan abun babu wanda zai yadda da ita cewar yarinyar lado ce, ba tare da ta ankara ba sai jin daka tayi tumm... *!!!* nan ta bi Ard'o da idanu yadda ya zage yana daka jaririyar tamkar yana daka gumba.

   "Kur'anin Allah 'yar nan ta halak ce, gashi nan da ranta garau..."

Cewar Sallau yana k'okarin fito da jaririyar da Ard'o ya gama kir6awa tamkar ma babu abinda aka yi mata dan yadda aka sata haka aka fito da ita subul...

Duk jama'ar gidan suka waro ido da tsananin mamaki kafin kowa ya maida hankalinshi ga Hafsatu dake kallon k'asa tana wasa da jelar gashin ganta. Inno ta dafe k'irji tana kallon Hafsatu cikin nuna sonjin k'arin bayani.

   "Hafsatu gamu ki gaya mana ya akai kika samu wannan cikin harkika haife shi bayan munsan lado bashi da mamora tsawan shekaru..."

Fad'in yabint tana daga nesa amma tana son jin tsegumi da jin kwakwaf...

     "Yabint *!* ai na gaya muku cewar jaririyar nan ta lado ce tunda gashi turmin kurtum ma ya shaida gaskiya..."

Hafsatu ta kuma fad'a nan da nan magan ganu suka ci gaba daga baku nan mutanan gidan k'asa-k'asa, Ard'o ya zabura tamkar zai tashi sama yana kallon Hafsatuwalle yace...,

    "Aradun Allah wannan maganar tak'i Hafsat akwai d'aure kai, muna son mu shaida zancenki tunda ga turmin kurtumi ya shaida amma ai lado bashi da lahiya bayya iya yin komai taya wanga lamari ya faru? Zamu je can shi gwadabniya dan mu shida."

Turmin kurtumi dad'add'an turmine tun zamanin iyaye da kakannin, al'adar garin ce in dai mace ta haihu dole ne aje a sashi ciki a kir6a dan tabbatar da cewar yaron ko yarinyar ta halak ce.  Tsafataccen turmi ne sannan kuma yarda da imanin da alummar garin suka yi da hakan shine yasa indai suka daka mutum a ciki be mutu ba to hakan ya tabbatar musu da cewar d'an halak ne duk kuwa da cewar tsakanin ma'auranat akwai sadaki amma duk sanda suka haihu sai an saka yaro a cikin turmin kurtumi ko kuma cikin wuta da take ci ganga-ganga tamkar za'a kuna karamin daji..."
    (Wannan ke nan)

Kus-kus aka farayi kafin inno ta furzar da huci mai zafi tace.

     "Ni dai kam Hafsatu zaman ki ba dai a d'aki naba. Ard'o sai dai ka sama masu inda zasu tsafa rayuwar su ni dai kam bada niba..."

Guri ya kaure da hayaniya kowa ya nuna badashi Hafsatu zata zauna ba, sallau yasa suka yi shiru Hafsatu na hawaye ganin kowa yak'i ta lauratu ta k'arasa tare da kama hannunta itama cikin kukan take mata magana k'asa-k'asa.

     "Umma ta kiyi shiru ki dena kuka, idan kowa ya guje ki ni ina tare daku kiyi hakuri Umma na..."

Kafin Hafsatu tayi magana sukaji muryar Ard'o na cewa.

     "Mukam dai Hafsatu sai dai ki zauna a rumfar Yafindo, amma damu da yaran mu babu ruwan mu daku karku shafa mana *Abunda ke 6oye* har sai randa munkaji gaskiya."

Nan da nan hayaniya ta kaure a cikin gidan Kafin kace me, tuni an watse daga gurin kowa ta kama harkar gaban shi ana ta yada magana lauratu taja hannun mahaifiyar ta suka shiga cikin d'akin Yafindo da aka basu shi. Babu koma cikin sai k'asan ma duk k'asa ce haka suka shiga lauratu ta cire mayafinta ta nunkashi tasa a k'asa sannan ta kwantar da yarinyar akai.

    "Umma ya kinka sa sunan jaririyar...?"

Tana hawaye jikinta na rawa ga jini sai zuba yake ta k'arasa gurin jaririyar tana shafa kanta tace "lauratu na sanya mata suna *Hafsat* Allah shi raya mana ita."

Lauratu tace "amin Umma....."


*[[ ]]*      *[[ ]]*

     *G*wadabniya *!*.... Sunan dake yi mishi yawo a cikin brain d'inshi kenan, mtww ya saki tsaki yafi sau ashirin ko sunan ya tuna ranshi 6aci yake baran tana idan ya tunu cewar shine zashi can d'in....,

    "Ma'aruf ya dai lafiya ko?" Madre ta tambaya bayan ta shigo cikin parlorn daga gani itama daga wajan aiki ta dawo.

    "Madre gobe zanyi tafiya zuwa katsina kan wani case da zanje nayi solving d'in shi..."

"Shine Ma'aruf ka zauna kanata faman 6acin rai kai d'aya?" Madre ke fad'in haka tana kokarin zama cikin d'aya daga kujerun da suka k'awata d'akin.

Shiru Ma'aruf yayi yana turo baki ya k'i kuma had'a Ido da ita Madre ta girgiza kai da mamakin shi cikin zuciyar ta tace.

     "To ka tashi kaje ka shirya mana ka zauna sai tunani kawai kake yi. Flight d'in nawa zaka bi..?"

A harzuk'e ya tashi tsaye fuskar shi a d'aure ya ce mata "Madre 8:00am." Yana fad'a be jiraci cewar ta ba yabar parlorn kamar zai tashi sama wajan fita suka yi karo da Sumayya amma ko ta kanta be biba ya wuce part d'inshi.

Bedroom ya wuce ya fa fad'a kan bed tare da rik'e kanshi me barazanar tsagewa sabida tsabar sara mishi da yake yi. Ya kusa 2hours a kwance kafin ya tashi ya koma dressing room ya fara shirya kayan shi. Har aka kira magrib sannan yayi alwala ya wuce masallaci dan gabatar da sallah, ana idarwa ya koma side d'inshi ya ci gaba da shiryawa har ya kammala ya koma parlorn shi ya zauna yana jin tsanar zuwa kauyan.

    "Yaya Ma'aruf Madre na kiranka." Sumayya ta fad'a cikin d'ar-d'ar tana kallon shi. "A'm coming."

Yace da ita ba tare da ya kalleta ba, kura mishi idanuwa tayi cike da tambayoyi uwa uba kaunar shi da soyayyar shi dake addabar rayuwarta ya d'ago tare da sauke mata uwar harara ta juya da gudu tabar d'akin.

Ko 2minit bata yiba sai gashi, zama yayi Madre ta dube shi tace, "kazo kayi denner Ma'aruf." Lokacin abban shi ya shigo duk suka yi welcoming nashi kafin suka wuce dining gaba d'aya.

Tsakurar abincin kawai yake kafin yace "Abba gobe zan wuce katsina akan mai Apf d'in nan by 8:00am jirgin zai tashi."

"Good my son, Allah ya bada sa'a I know my son is a nice musamman akan aikin shi, Allah ya baka sa'a my son."

Madre da Ma'aruf suka had'a baki wajan cewa "amin..." Sumayya ta saci kallon shi suka had'a ido ta sakar mai kayataccen murmushi ya harareta tare da mikewa yace ya koshi sannan yabar side d'in zuwa nashi.

Washe gari yana gama shiryawa wajan 7:00am ya fito dan tafiya airport cikin shigar shi ta suit milk color abinka da beauty sai yayi bala'in kyau. Room din Abba ya shiga tare suka fito suka had'o da Madre a kitchen ta fito hannunta rik'e da wata kyakyawar leda ta mika mai suka rakoshi har inda drive ke jiranshi suna ta mai fatan alkairi da samun nasara, jiyayi tamkar karya tafi ya barsu amma Abba ya karfafa mai gwaiwa suna d'aga mai hannu har suka bar compound d'in.

Sumayya kam bata san ya tafi ba sabida tsabar baccin da take yi, sai da ta farka wajan 11:15am sannan take tambaya Madre tace "ya tafi kilama sun sauka yanzu....."








*FEEDOHM*💞
&
*HAJJA CE*👈
[5:54PM, 11/24/2017] 💧💧 Feedohm💞: 💧💧 *ABUNDA KE BOY'E……*
        《Almost True Life Story》

                   🍁🍁
                      💧

© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


        *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*
   *&*
*_K.A.S Precious HAJJA CE👈_*

*SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《Ummana》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
 *Da dukkan masu suna HAFSAT dake duniyarmu*


   page *11-12*



Tunda asuba Lauratu ta tashi fita tsakar gida ta iske Jummai na surfen geron da za'ayi karin kumallo dashi yau "Gwaggo jumma Ina kwana?ta fada tare da dukawa har kasa

  Yatsina fuska tayi tare da tabe wargajejen bakinta sannan tace "Lahiya"
Mikewa Lauratun tayi ta nufi murhu ta debo kakare ta hada wuta sannan ta dauki tukunya ta nufi randa zata debi ruwa……

  Da Sauri jummai ta matso tana fadin "Ke ke tsaya ruwan me zaki diba kuma?

  "Ummana zan daurawa ruwan wanka……"

 Wani kallo ta watsa mata sannan tace "To bada ruwan gidan nan ba wallahi don babu shegen da yace ta haihu acikin mu……"

  "Haba Gwaggo Jumma tunda fa ta haihu batayi wanka ba ,dan Allah ki sammani na diba ko ya yane ta samu taji karfin jikinta "ta karashe maganar tana kallon kasa idanunta cike da kwallah……

  "Kar ta ji karfin jikinta lauratu!idan abun ya dameki kije ki debo mata a rafi mana ina jin kinsan inda zaki debo mata!Muma mazajenmu suka debo mana don muyi amfani dasu ba dan ayiwa Shegiya wanka ba……!ta karashe maganar tana tada jijiyoyin wuya

  Juyawa tayi ta dauki tulu ta fita ba tare da tace komae ba sae dae zuciyarta dake tafasa kamar ta kone……Da tsaki Jummai ta raka tana fadin "Shegu masu abun kunya"

  Cikin Sauri ta debo ruwan ta dawo ta sake hada wata wutar har sae da sukayi zafi sannan ta leka bangaren Inno ta aro katuwar ruba ta juye rabi……
Sauran kuma ta zuba a bokiti ta kai ban daki……

Jaririyar ta amsa daga hannu Umman tace "Umma ki tashi kije kiyi wankan na kai maki ruwa a bandaki……"
 A Hankali tace "Nagode ……"sannan ta mike ta fita tayo nata wankan……Jaririyar ta saka cikin ruwan ta gasata sossa……

  Tana gama mata wankan ta ladeta cikin kallabinta tana kallonta ,Tausayin yarinya ya kamata sosae ganin ko Dan kamfai bata dashi,Daukarta tayi ta goya sannan ta fita daga gidan……

Gidan mai unguwa ta shiga ta tambaya ko akwae Surfe,Cikin sa'a suka bata masara tiya goma suka ce a surfa zasuyi tuwon sadaka da ita ……

  Haka ta ja masaran ta koma gida lokacin mutanen gidan sae karin kumallo suke ,Bukkarsu ta nufa ta iske Umman a zaune ba'a kawo mata komae ba ,hawaye taji suna niyyar zubo mata ta fita da sauri tana tambayar Jummai ina abun karin kumallon su……
Matan gidan suka dauki sowa suna fadin "Ashe har abinci gareku bayan abun kunyar da kuka dauko mana "
Wata ta amshe da fadin "Shi kwarton uwar taki bai kawo maku komae ba?ko bai san ta haihe mashi diya ba ?

  Jummai ta amshe da fadin "Ke nifa ban yarda da yadda Ard'o ya k'irba yarinyar nan ba! don wallahi kadan yake saka tabaryar a ciki ko diyar bata tabawa"
  "Nima wallahi abunda nake son fada kenan,kawae raina mana wayau yayi don ya fahimci shegiya ce……"

Inno dake tsaye tana jinsu ta kira lauratu ta mika mata nata abun karin kumallon ta juya a sanyaye ta koma dakinta ……
Lauratu kam Umma ta kaiwa abun karin kumallon ta juya zata fita ta kira ta tace tazo ta zauna taci ……
Duk da irin yunwar da take ji murmushi tayi tace "Nasha nawa Umma"

 Ta dade tana kallonta sannan ta gyada mata kai tana share hawayen da suka zubo mata ,Da sauri lauratun ta fita ta fara surfan masarar ……
Kafin rana ta take ta gama surfewa har an bata kudinta naira d'ari ……Jaririyar ta kwanto tana fadin "Umma ki bata abinci yanzu zan fita da ita……"

  Cikin sanyin jiki tace "Ina zaku je Lauratu?
  "Umma dan kamfai zan sawo mata da riga a Gwadabniya nan garin ba'a siyarwa……"

  "Ina kika samu kudi?
  "Umma surfe nayi yanzu"ta fada tana rike kafar Jaririyar……
Shiru tayi tana kallonta har sae da jaririyar ta dauke kai daga MaMan sanna lauratun ta dauketa suka tafi……

【】

 *M*a'aruf yana isowa aka bashi Guard mace sannan suka nufi Ward din cikin HLuxur……,Focal person suka dauka sannan suka nufi Gwadabniya……Ganin yarda suke keta daji ya sashi sakin tsaki lokaci lokaci ,Bai taba tunanin akwae mutanen da ke rayuwa ba a wannan dajin ……
Saukin suma Hluxury ce ba'a cika gane wahalar tafiya da ita ba don bata raina tudu da gangare ……
Gidan Mai unguwa suka sauka Ma'aruf na cikin motar bai fito ba .Mai unguwar ya leko yana washe jajjayen hakoranshi ,daga mashi hannu kawae yayi sannan ya bude motar ya fito Guard dinshi na a bayanshi……

  Gidn Malan Lado suka nufa tare da dandazon yaron da suka zagayesu……Har cikin bukkar ya Shiga ya dubashi sannan ya fito yana karewa ilahirin mutanen dake gidan kallo ……
Uban wari ke fita ta ko'ina ga ruwan da ya kwanta tsakar gida ……Dan karamin tsaki ya sake ja lokacin da Maitafasa ta iso gabanshi tana fadin "Yaro yaya kaga jikin nashi?dan Allah ku taimaka ya warke ko ya dauki Fansa a kan cin amanar da matarshi ta mashi ……"

 Banza ya mata ya juyar da kai gefe guda tare da fita daga gidan suka tsaya jikin motar yanawa Focal person magana ……

Lokacin Lauratu ta iso garin tana hango dandazon yaran da matan aure da itama ta kutsa kai cikinsu ta tsaya gaban Ma'aruf din tana sauraren abunda yake fada duk da dai ba ganewa take ba saboda mafi maganarshi turanci yafi yawa ……

Uban Ihu Jaririyar ta saki tana kuka …
Kallonta yayi ya dauke kai saboda baya kaunar kuka yana fadin "Bar nan gurin……"Fuska a daure

  "Ina Saurarenka ne Bature……"ta fada tana jijjiga yarinyar,Cigaba da kukan jaririyar tayi tana mutsu mutsu a bayanta ……Kukan ya fara isarshi cikin tsawa yace "Shut up ki bar nan gurin……"

  Dariya tayi tace "Ba sunana Shutu ba Sunana lauratu!yar kanwata kuma Hafsatu……"

  "Hafsah……"ya fada yana kallonta "Kawota mu gani……"ya karashe maganar tare da mika mata hannu

Da mai unguwa ake kokarin kwanto yariyar tare da mika mashi"Me yasa ba'a saka mata kaya ba?ya fada idonshi na kan yarinyar……

"Bata dasu Bature shegiya ce ita ce warda Uwarta taci amanar mijinta da ka dubo yanzu……"Cewar mai tafasa sannan ta kalli lauratu tace "Karbeta ki bar nan tun kafin na fasa maki kai……"

  Fitinannen kallo ya watsawa Mai tafasar sannan ya fito da kudi akalla sunkai 50k ya mikawa Focal person din yace "Ka sayar mata duk abunda ya dace……"Mikawa lauratun ita yayi ya bude mota ya shiga Sannan Focal person din ya karbo sample Urine din da akace a kawo suka shiga motar suka tafi ……

  Mai tafasa da sauran mutanen garin Mamaki ya hana su magana har sae da suka bar ganin kurar motar su sannan Mai tafasar ta juyo da niyar Zazzagawa Lauratun ruwan masifa amma ta nemeta ta rasa……

Lauratu kam bayan gida ta zagayo ta shigo ta karare ta shige bukkar Malan Lado ……Kwance ta iskeshi kamar kullun idonshi a rufe sae dae hawayen dake zubowa……kwanto jaririyar tayi ta daura mashi saman kirji ,ya dube ido da sauri yana kallonsu ,lokaci guda ya fara gyada kai yana murmushi dake dauke da hawaye yana kallon yarinyar ……
Jikin lauratun yayi sanyi tace "Baffa yarinyar ka ce ko?

Gyada kai yake da sauri yana murmushi ,Itama murmushi tayi ta janyo kwanon furan da ta gani gefe tana fadin "Baffa ka sha?

  Girgiza mata kai yayi yayin da murmushin fuskarshi ya bace ,Shiru tayi sannan ta dauke diyar daga jikinshi ta dago kanshi tana bashi furar……
Sae da yasha sossae Sannan Jaririyar ta tsangare da kukan da yasa Mai tafasa da kumdum suka nufo bukkar suna fadin "Wane Shegene anan ciki?

Kwantar dashi tayi da sauri ta dauki jaririyar ta fice ta yar kofar dake bayan bukkar ta bi ta karare ta fita ,Suna shigowa suka ga babu kowa……

Kundum tace "Lado hala wannan Shegiyar yarinyar ce ta shigo……"



*HAJJA CE👈*
  &
*FEEDOHM💞*
[5:03PM, 11/25/2017] 💧💧 Feedohm💞: 💧💧 *ABUNDA KE BOY'E……*
        《Almost True Life Story》

                   🍁🍁
                      💧

© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


        *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*
&
*_K.A.S Precious HAJJA CE*👈


*SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《Ummana》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
 *Da dukkan masu suna HAFSAT dake duniyar mu*


        Page *13-14*

    *S*hiru yayi ba tare da yayi magana sai faman binsu da kallo yake har suka fita suna wa lauratu masifa ga bak'in cikin ganin uban kud'in da aka bayar wai a siyama jaririya kaya.

"Kur'anin Allah ko Mai-tafasa? Ina tausayin Hafsatuwalle duk ranar da lado ya samu sauk'i. Cewar kundum tana kokarin fita daga gidan gashi daga ita sai karigirji da zanin tsohowar atamfa wanda yaji dunyi ta d'ora akanta ko yaya ta d'aga hannu gashin hammata ne cacim tamkar zakayi kitso.

"Humm *!* kaji ki Kundum da wani zance, yo ce miki aka yi yadda zai yi? Jira kawai nake aradun Allah yaji sauki har gida zamu je ya tona mata asiri, dan taga ba magana yake yiba shine zata mai sharri muguwa kawai."

"Mudai muna jiran ganin irin hukuncin lado, dan a lokacin ne *Abunda ke b'oye* zai hito hili..."
    Kundum Tana fad'a tabar gidan da ragowar guntun gulman ta, lado kam yana ciki kwance yana jiyo su ji yake tamkar ya tashi amma ba dama hawaye suka zubo mai kafin kuma yayi murmushi yana kallon kirjinshi dai-dai inda laurtu ta d'ora mai jaririyar.

*{{ }}       {{ }}*

    Lauratu na shiga kauyan su da farin ciki dan har tama manta da zance wani 6acin rai sai da tashiga gidan su taji fad'uwar gaba ta k'arasa cikin rumfar su.

A zaune ta ga Umman ta tayi ta gumi wanda daga gani tayi nisa cikin tunani, duk sallamar da lauratu keyi Umma bata jita ba sai da ta k'arasa kusa da ita tare da janye hannun ta wanda ta tallafi habarta dashi tace "Umma na lahiya ko?" Kallon lauratu tayi tare da k'ak'alo murmushi wanda be kai cikin zuciyar taba, "me zata cewa lauratu bayan duk tunanin ta yana kan yadda taga tun yanzu ana muzguna musu *!* ana kyarara su tamkar tumaki, koda yake yanzu tumakin su sun fisu daraja da kima a idanun mutanan gidan." Umma Hafsatu ta fad'a cikin zuciyar ta, ganin irin kallon tuhumar da lauratu ke yi mata ne yasa ta kara wani murmushi cikin sanyin murya tana kallon Hafsat dake hannunta tace.

"Ba komai lauratu ina nan ina tunanin ku karkuje wasu suyi muku wani abun. Har kin samo mata kamfai d'in?

Umma ta fad'a cikin yana yi na bagarar da tunanin lauratu da ta kafeta da manyan idanuwanta. Zama lauratu tayi akan langa-langan data kwana akai jiya sai faman k'ara yake k'arass-k'arass ta bud'e guntun d'ankwalin da ta nad'e Hafsat dashi tana nunawa Umma kanfan (pant) da ta sai mata tare da cewa.

"Eh Umma na samo kuma munje gidan Mai-tafasa har muka tarar wani bature mai kyau yazo yana duba Baffa. Sannan Umma ya bada kud'i yace a siyawa Hafsat kaya amma banga mutumin ba sabida na zaga gurin Baffa har yaga Hafsat yayi murna."

Hirarsu suka yi ba tare da kowa ya lek'osu ba. Ganin rana tayi ne yasa su fitowa tsakar gida dan su kamawa mutanan gidan aiki. Da sauri Bultuwa ta janye kwanan garin dake gaban ta ganin Umma na kokarin kar6a dan ta tayi tankad'an cikin nuna kyama Bultuwa na sosa cikin hancinta tace.

"Kaunan Hafsatuwalle ki bani guri da wannan kazamin jikin naki. A kul *!* na sake ganin kinzo wai da nufin ki kamamin aiki na bana so." Cak... *!* Umma ta tsaya tana mata kallan mamaki lauratu ta sunkuyar da kai cikin takaicin ganin yadda ake musu wulakanci Mai-aya dake rik'e da tukunya tace.

"Aikuwa dai gara kiyi kayanki kar a goga miki cikin kato kema wataran kiyi." Wata mata itama dake gefe guda tana yiwa yarinyarta tsifa gashin yarinyar jawur kamar anrina shi ga uban kasa akai amma jira ake a tsefe ayi kitso ba tare da an wanke ba tace, "Bultuwa kinyi dai-dai tallahin Allah k'ara da kika d'auke kayanki."

Jin maganganu sunyi yawa ne yasa Umma da lauratu komawa cikin rumfar su, zama suka yi akan mayafin lauratu da ya zamar musu kamar da6en kasa Umma na kuka k'asa-k'asa ta kalli lauratu da itama hawayan take yi "lauratu kiyi hakuri kuma ki yadda dani cewar Hafsat ta lado ce k'anwarki ce karki biyewa bakin mutanan nan...."

Lauratu ta gir-giza kai sannan tace, "Umma rik'eta naje na dawo yanzu." Kar6arta Umma tayi tana kallon lauratu "ina zaki kuma da rana haka Laure???"

"Umma gidan mai-unguwa zani ana bada tuwon sadaka nima bari naje na kar6o mana." Tana fad'ar haka ta fita bata jira cewar Umman ba.....

*{{ }}*

Yana komawa cikin hotel d'in da aka kama mai ya cire kayan jikin shi tare da shigewa toilet, wanka ya dingayi sabida shi a tunanin shi ya kwaso wannan warin da yaji a gidan da suka je, sai da ya tabbatar ya cud'a ko'ina sannan yayi alwala yafito jikin shi d'aure da towel hannunshi da small one ya k'arasa jikin dressing mirrow yana goge jikin shi mai d'auke da kwantaccen gashi mai yawa a k'irjin shi da hannayen shi da kafafuwa.

Tsaki yayi ta faman saki yana tuno yadda yaga suna shiga kauyen daga manya har yara dukun-dukun dasu hanci duk majina sunyi fututu kamar suna birgima a jar kasa, suna hango mota kowa ya fara gudun shiga gida, yaji haushi sosai sai kace wasu 6arayi.

Zama yayi akan stool ya fara shafa k'amsassun lotions a jikin shi, murmushi yayi wanda yasa fararan hak'oran shi bayyana masu kama da kankara lokacin da ya tuno sanda ya ce "shut up *!*, tace "ba sunana Shatu ba sunana lauratu kanwata kuma Hafsatu.."

A hankali cikin sauti k'asa-k'asa ya furta "village girl.." Lokacin ya kammala shafa duk wani abu da yake bukata sannan ya doshi drower ya janyo boxer short da vest ya sanya tare da d'aukar phone d'inshi yayi dailing numbern Madre.

Tana shiga yaji muryar Sumayya cikin d'oki, kafin tayi magana yayi saurin katseta da cewa "where is my Madre? Please ban son wani magana ki ba ta ina son yin magana da ita." Ranta ya 6aci tayi kamar zata yi kuka tace.

"Amma Yaya Ma'aruf me yasa baza ka bari mu gaisa ba? Sai kace ba kanwanka ba kayi ta min haka?"

Tsaki yayi tare da lumshe idanuwa a hankali yace "to naji mu gaisa amma bana son k'orafi." Bata yi fushi ba duk da taso tayi mai korafin me yasa ya tafi basu yi sallama ba amma ya hana hakan yasa ta cewa.

"Ina yini ya aiki? Normal." Kawai yace mata yayi shiru jin haka yasa tace mai "Yaya ga Madre d'in." Tare da mik'a mata ita kuma ta koma gefe tana jin Madre nayi mai fad'a akan yadda yake nuna cewar baya son zuwa kauyan wai basa wanka shi kanshi marar lafiyar yana bukatar gyara, nan tayi ta nuna mai cewar duk d'aya suke sai wanda yafi wani tsoran Allah.










*FEEDOHM*💞
&
*HAJJA CE*👈
[2:23AM, 11/26/2017] 💧💧 Feedohm💞: 💧💧 *ABUNDA KE BOY'E……*
        《Almost True Life Story》

                   🍁🍁
                      💧

© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


        *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*
   *&*
*_K.A.S Precious HAJJA CE👈_*

*SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《Ummana》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
 *Da dukkan masu suna HAFSAT dake duniyarmu*


    Page *15-16*



*M*aganganun Madre su shigesu sosae ……Sun dade suna waya sannan ta yanke , Lokacin sumayya na zaune kusa da ita ta kalleta tace "Madre wae Yaya Ma'aruf bara yayi aure bane……?

 Dariya Madre tayi sannan tace "Wane irin Aure Sumayya?Duka Ma'aruf din nawa yake?He's 24yrs idan wannan month din ya mutu,Kawae Allah ne ya bashi sa'ar rayuwa……"

 Bata Fuska tayi tana fadin "Amma Madre ai yana da abunda zai rike mata yanzu!kuma wallahi baki ga yarda yan mata ke sonshi ba a waje,don babu wanda zaice bai kai 30years ba gaskia a nema masa yarinya cikin family dinmu yayi aure kawae……!

  Dariya kawae Madre din tayi ba tare da tace mata komae ba……Ita kam bara ta kashe danta ba tun yana yaronshi tafi son shekarun shi su kai 32 sannan yayi auren don lokacin ta tabbata ya san yarda zai zauna da Mace ……

  Sumayya kam haushi taji da Madre bata yarda da zancenta ba Ita idan san samu ne tafi son da ta gama secondary School a mata aure dashi tunda yanzu SS3 Take domin a tsarin rayuwarta babu batun cigaba da karatu……

*Ma'aruf*

Ma'aruf Muhammed Ma'aruf shine cikakken sunanshi !D'and'a ne Ga Alh M Ma'aruf da Hajiya Hafsat Madre!Suna Zaune a garin Kaduna Unguwar Sarki Mahaifinshi Babban Dan kasuwane yana da company a Ibadan da suke fitar da sweet ta Splash sannan yana da wani a kaduna da suke buga robobi……Yaransu biyu Maryam ce babba sae Ma'aruf !amma ita tayi aure har da yaranta biyu……Ya tashi cikin gata da kulawa tare da tsantsar addini daga gurin iyayenshi da yar'uwarshi ,Yana da shekara Sha bakwae ya gama secondary school dinshi cikin shekara daya ya samu admission kasar Egypt cikin Cairo anan yayi karatunshi tsawon shekara 4 bangaren Laboratory sannan ya dawo Nigeria! Allah ya bashi sa'ar rayuwa ya samu aiki a World health organization a matsayin WHO Consultant……!

  Sumayya yarinyar k'anin Madre ce tun bayan rasuwar Babanta ta dawo hannun Madre da zama, tun lokacin da ta dawo ta dauki Son duniya ta daurawa Ma'aruf  bata da wani tunani sae tunanin ta aureshi……Shi kanshi Ma'aruf din ya sani saboda tasha fada mashi amma ko kallonta bayya yi……!

【】

  Ma'aruf Bayan Madre ta yanke wayar Ya dauki siririn farin glass dinshi ya saka sannan ya janyo laptop ya duk'ufa yana yan bincike ……

Focal person din kuwa suna rabuwa da Ma'aruf LGA meeting suka shiga sae da suka gama sannan ya shiga central market ,yan kayan jarirai ya sawo mata da basu wuce na 10k ba sannan ya dawo ya kawo ma mai ungua yace ya kai masu ……

Mai ungua ma sae da ya tsintarwa yarinyarshi sannan ya taka da kanshi ya kaimasu ,Lauratu ta amsa tare da godiya sannan ta kaima Umman nata……

《》《》《》

Rayuwa su Hafsuwalle suke cikin k'yara da tsangwama Dukkan gidan babu mai zuwa kusa dasu hatta yara k'anana an hanasu zuwa inda suke zaune ……Sae dae kullun Lauratu zata dauki kanwarta suje Gurin Baffa a sace ba tare da kowa ya sani ba……

Haka Hafsuwalle ma takan Saci jiki taje ta gano mijinta ba tare da kowa ya sani ba wani sa'in sae taje take bashi abinci sannan ta gyara mashi inda yake kwanciya……

  Abinci da zasu ci ya fara gagaran su don Sau daya ake basu abinci a rana shima sae da daddare kuma ko Lauratun bara ya isa ba bare su biyu……don haka Hafsuwallen da Lauratu suka dage suna surfen kudi……da kudin suke samu su sayi gero da yar masara suyi abinci duk ranar da basu da abunda zasu ci haka zasu wuni da yunwa ko da za'a zubar da abinci gabansu……K'ara ma Inno wani sa'in tana kula dasu ……Abunka ga Uwa sae ta fara tausayinsu ta je ta samu Ard'o tace ya masa kamata suje gidansu Malan Lado suji me ake ciki……

  Bai musa mata ba ya shirya shi da Hafsuwallen da jaririyarta suka tafi ……Suna shiga garin yara suka taresu da "Ga Gayyar Tsiya……"

  Ard'o Ya kalli Hafsuwallen a sanyaye jin abunda yaran garin suke fada ,Duk'ar da kai tayi k'asa tare da gyara goyonta ,Cikin k'ank'ani lokaci mutane suka fara fitowa daga gidanjensu don ganin su waye Gayyar tsiyar ……

  "Lallae Gayyar Tsiya ……"Cewar Kundum tare da komawa cikin gida ta samu Mai tafasa Da ke zaune tana tsige tafasarta tace "Abun kunya baya karewa su Hafsuwalle "

A Zafafe Mai tafasa tace "Ke kundum ni bana son munafunci!dan kinga bana son ko jin sunan Hafsuwalle shine da gulmarki ta motsa sae ki dinga k'ira man ita ……"

  Watsa hannu tayi tana fadin "A Hayye ……Maida wukar Mai tafasa!Hafsuwalle da tsohunta na gani sun nufo gidan ga Shi yasa na zo na fada maki don ki tanadi kalamun ci masu mutunci……"

  Zumbur ta mike tare da hankad'e kwaryar tafasar ta zube kasa tayi waje tana fadin "Da kwarankwatsa yau garinnan sae nayi kisan kai !Banda dibar Albarka bayan cin amanarmu da akayi shine za'a kwaso kafufuwa ace za'a shigo mana gida!Uban me ya kawoku kai kuma tsohon banza ka kwaso lauyayyen wuyanka kamar rakumi ka taso yarinya gaba me zaku fada mana!

  Tsaye sukayi kamar an dasa kara suna kallonta har ta karaso gaban Ard'o ta tsaya tana watsa hannuwa baya"Na ce me ya kawoku kuma? ……Lallae Ard'o ka cika babban banza tunda har baka ji kunyar shigowa garinmu ba ……Da kwarankwasa kunji kunya maciya amana kawae……"

Danne Fushin shi yayi yana fadin "Kiyi hakuri Tsohuwa mu shiga ciki sae muyi magana……"

Hannunta ta watsa saman fuskarshi"Anki a shiga d'in Tsohon kawae marasa mutunci watsatstsu masu gadon abun kunya!Mu shiga ciki kayi mani me yan iska?wallahi Ard'o ni da ku sae rashin mutunci a tsakani "

 Juyawa yayi a fusace yana kallon Hafsuwalle "Kinji Kunya Hafsatu kin saka an wulakantani a inda ba'a isa ba, tur dake!

Kuka ta saki da karfi tana girgiza mashi kai "Ka Gafarceni Ard'o Wallahi ban aikata abunda suke zargi ba"

 "Tur Dake Hafsatu!Me yasa lokacin da Ladon ya nemeki baki nuna mashi aibun da abun zai haifar ba kin biye mashi kin saka an wulakanta mu !kin haifar mana da abun kunya a zuri'armu wa zai yarda d'iyar Lado ce ……!

  Kundum tace "Can ta matse maku munafukai Sae a k'ara gaba Don Mai tafasa ba sakarai bace da zata karbi Shege!

  "Bana son fa munafunci Kundum idan ina tsiyata ki daina saka man wagegen bakinki……!Mai tafasa ta fada tana watsa hannu gaba sannan ta shige gidan tana fadin "Wani kukan ma Sai ranar da Ladona ya warke……"





*HAJJA CE👈*
   *&*
*FEEDOHM💞*
[2:28AM, 11/26/2017] 💧💧 Feedohm💞: 💧 *ABUNDA KE BOY'E……*
        《Almost True Life Story》

                   🍁🍁
                      💧

© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


        *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*
   *&*
*_K.A.S Precious HAJJA CE👈_*

*SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《Ummana》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
 *Da dukkan masu suna HAFSAT dake duniyarmu*


    Page *17-18*





Juyawa sukayi Hafsatun na kuka suka tafi ……Sauran mutanen garin suka bisu da ihu tare da zagi har suka bar garin ……

  Koda suka koma Gida Ard'o duka mutanen gidan ya tara tsakar gida a fusace yace "Ni kam dae na yafe Hafsatu cikin yarana don haifi yarinyar da zata saka a wulakanta ni ba……"

 Kuka Hafsatun take kamar ranta zai fita yayin da ta duk'a saman guiwarta tana bashi hakuri amma sam yak'i kulata ya juya zai tafi ……Inno ta kasa jurewa ta tareshi a sanyaye tana fadin "Ard'o ka saurareta dan girman Allah!ka gwada wanga jaririya ka gane ta halak ce mai yasa zamu k'ita?

  "Saboda iyayenta yarinyar basu karbeta kuma nima na kasa gasgata Hafsatu akan Hafsatu yau aka wulakanta ni a ci man zarafi taya zan karbi Hafsatu?Ban hana Hafsatu rayuwa a gidana ba amma ko k'wayar hatsi ban yarje a bata ba……" Yana gama fadar haka ya juya ya bar gidan

【】

  Bayan Sati biyu Ma'aruf ya bayar da Magunguna aka kawo ma Malan Ladon kafin su gama bincikensu a kanshi sannan ya koma gida ……

Tarba ya samu sosae gurin Madre da Abba……Sumayya kam sai iyayi take amma ya nuna bai san tanayi ba ……
Sae da ya huta sannan ya kalli Madre yana bata fuska yace "Madre karatu zan koma wallahi wannan aikin duk karyace an rigaya anyi eradicating cutar a nigeria hakanan muke wa mutane karya……"

Hararanshi tayi tace "Bana son haka Ma'aruf aikin naka kake karyata?

 Langwabe kai yayi yace "Madre gaskia na fada ni karatu zan koma"
 "Kace karatu zaka koma Ma'aruf Simple!
 Lumshe ido yayi yace "Eh Madre
Murmushi tayi tana girgiza kai sannan ta janyo wani littafi ta mika mashi tana fadin "Ka duba wannan littafin akwae addu'o'i da yawa a ciki sannan yau kayi istihara ka nemi zabin Allah akan karatun ko barinshi Kafin na Fada Abbanka ……"

  "Thank you Madre……"ya fada yana murmushi
Daga haka suka cigaba da firansu……

  Bayan yayi istihara ya fadawa Madre din cewa yana tunanin Karatun nashi alkhairine Ita da kanta ta fadawa Abbanshi……Abunka da masu kudi cikin kankanin lokaci aka shirya tafiyarshi kasar India ……Kuka kam Sumayya tasha shi kamar zata mutu……

【】

Su Hafsuwalle rayu suka fara yau da dad'i gobe ba dad'i Har Hafsat K'arama ta fara wayau dukan gidan daga Lauratu Sae Umma ke daukarta tun tana ganin mutanen gidan tana mika masu hannu alamun su dauketa har ta daina sae dae idan Lauratu na aiki ta rarrafa kusa da katuwar bishiyar kukar dake gaban gidansu ta zauna anan zatayi wasanta ita kadae har sae lokacin da Lauratun ko Umman suka gama aikinsu sannan su dauketa su shigar da ita gida ……Wani Sa'in har a gama Magrib tana zaune gurin sannan ko zatayi kukan duniya babu wanda zai kulata daga iyalen gida bare ya dauketa ……Gashi Allah ya zuba mata wani irin kyau kamar ita tayi kanta da farin jini ga mutanen waje amma na gidansu basu kaunarta……

Lokaci na kara ja Har Hafsa karama tayi shekara hudu da haihuwa lokacin ta fara magana sossae sae dae bata cika surutu ba idan kaji tana magana to da Lauratu takeyi……bata kula ko wane yaro kamar yarda babu mai kulata,Duk wani hidimarta ta ya koma hannun Lauratu abunda ke hadata da Ummanta idan sunzo bacci!amma zata wuni tana wasanta a bakin bishiyar kukar ita kadae saboda duk sun hana yara tsaranta wasa da ita……

Cikin lokacin kankani ta gane wani irin kuka na masifa duk in lokacin Magrib yayi haka zatayi ta ihu tana zambarwa tare da mike mike kamar zata shid'e ……Tun abun baya damu Umman har ya fara damunta yarinya zata wuni tana wasanta amma da Magrib tayi ta gama walwala har sae dare ya take !wani sa'in ma haka za'a wuni ba'a ganta ba Sae gab da mangrib sannan Lauratun Zata ganta zaune kusa da katuwar kukar dake gefen gidan……

Cikin Dan lokacin Sallau yaron kanwar Ard'o ya nuna yana son Lauratu da aure ……Dukkan mutanen gidan kin amincewa sukayi wai kada a goga masu abun kunya……Amma da yake Tsaye yake ya nuna babu wanda ya isa ya hanashi auren Lauratun tunda ba ita ce tayi abun kunyar ba……
Ba dan anso ba aka saka baikon Lauratu da Sallau……Da yake gidan gandu ne anan ya yanki fili ya yi karamin dakinshi ……

  Lauratu na Zaune tana wanke kwanunkan da sukayi amfani dasu, Ummansu kuma tana surfa masara……Mutanen gidan kowa na aikin gabanshi masu yada masu magana nayi masu habaici ma nayi amma babu wanda ya kulasu  ……

Hafsa karama na zaune bakin bishiya tayi bud'u bud'u da jikinta ko riga babu a jikinta d'iyar kara ta hada tana saka mata kayan leda hankalinta kwance sae murumushi take zubawa kamar tana wasa da mutane……

Jummai ta gifta ta gabanta tare da kwallo da kayan wasanta tana hararanta tace "Shegiyar yarinya ita ba gidan ubanta ba amma ta cika mana gida da tarkacen hauka…… "

Dagowa tayi tana hararanta cikin maganar da bata biye mata baki ba tace "An Dummai Allah ya isa ……"

  Finciko ta tayi ta wanka mata mari sannan tace "Shegiya mara kunya ni zaki ma Allah ya isa to k'ara man Allah ya isan ki ga yarda zanyi dake a gidanki"

Dukar da kai tayi tana surutai kasa kasa tare da hararan jummai ta kasan ido, lauratu tayi saurin zuwa gurin ta kamata tana fadin "Me yasa kika mata Allah ya isa K'arama?

 Shiru tayi tana kallon katon cikin Jummai sannan tace"Ba abincin amarya bane ta zubar!Kuma sae na fadawa Ayd'o Mijinki ya satar mashi kaza kun dafa a daki kun cinye"

  "Eyeh Ni zaki jawa Sharri k'arama"Jummai ta fada tare da fiddo idanu waje sannan ta bar gurin buguzum buguzum tana waigensu kai da gani kasan bata da gaskia……

 Da Kallo Lauratu ta bita sannan ta ja hannun Hafsah din suka nufi inda suke aje ruwa tana fadin "Kar na sake jin wannan maganar kinji ko ?sannan waya fada maki Sun Saci Kazar Ard'o K'arama?

  Kallon lauratun tayi da idanuwanta da suka rine suka koma jawur dasu wanda har lauratun sae da ta tsorata ta saketa tare da ja baya sannan tace tace "Ni na gani kuma idan karya nayi ki duba cikinta akwae sauran naman da bai narke ba……"

 Dafe kirji tayi tare da ja baya tana kallon Hafsa tace "Na Shiga uku ni Lauratu ya za'ayi naga cikin mutun K'arama ?

  Shiru ta mata ta debi ruwa tana sha lokaci guda idanuwan suka washe suka koma fararensu tas sannan ta nufi bukkarsu ta bar Lauratun tsaye tana kallonta……
Da Sauri ta nufi gurin Ummansu tana fadin "Umma kin ga Idon K'arama kuwa?

 A Sanyaye tace "Me ya sameta?
Zatayi magana ta hango Hafsa din tana niyar Fita daga gidan bayanta ta bi tana kwala mata kira amma ko ta juyo…… har sae da ta kai bakin bishiyar  da take zama sannan ta zauna ta dauki wani katon Dutse ta daura a cinya tana girgiza kafa tare da murmushi……

  Tsaye tayi tana kallonta sannan ta koma gida ta cigaba da aikinta sai dae duk jikinta yayi sanyi ……Sae da suka gama abinci sannan ta je da kanta ta janyota suka shiga bukkar su suka zauna……
Daga kai tayi ta kalli Ummansu Tace "Yaya Lauratu Baffa nake son gani……"




*HAJJA CE👈*
      *&*
*FEEDOHM💞*
[7:31PM, 11/26/2017] 💧💧 Feedohm💞: 💧💧 *ABUNDA KE BOY'E……*
        《Almost True Life Story》

                   🍁🍁
                      💧

© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


        *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*
&
*_K.A.S Precious Hajja ce*👈


*SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《Ummana》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
 *Da dukkan masu suna HAFSAT dake duniyar mu*


        Page *19-20*


    *D*asauri lauratu ta kalli k'arama tana zaro idanuwa cikin tsananin mamaki ganin dare ne amma take cewa gurin baffa zata, cikin tsoro wanda ya bayyana karara a fuskar lauratu tace cikin sanyi, "K'arama ya zamu je can gwadabniya cikin daran nan tsakani da Allah?"

Baki ta turo cikin shagwa6a, kafin kace me tuni fuskar hafsat k'arama ta sauya tayi saurin kwantawa akan zanin dake shimfid'e a k'asa inda suke kwana tayi shiru tamkar me bacci Umma da lauratu suna ta tashinta amma tayi kamar tana bacci hakan yasa lauratu dubawa taga lallai baccin take sannan ta kalli Umma tace "Umma 'yar rigimar Mu tayi bacci muma Mu kwanta yadda zamu tashi da wuri muyi sissikar nan."
   Daga kwancen da suke suka yi 'yar hira kad'an abinka da gajiyayyu tuni bacci ya d'auke su gaba d'aya. Jin saukar numfashin sune yasa Hafsat saurin mikewa sai faman zazzare idanuwa take gashi yadda take yi d'in tamkar wata babba, sim-sim-sim ta fito daga d'akin ba tare da kowa ya ganta tayi kauyan gwadabniya harda 'yar wakar ta.

Sai da ta fara lekawa d'akin mai-tafasa, ganinta tayi tayi bajebaje akan garu tana bacci baki sake hanci a sama sannan ta juya ta shiga inda lado ke kwance da fitilar kwai a kunne wadda take shirin mutuwa sabida k'arancin kananzir. Kallon fitilar kawai k'arama tayi sai ga haske ya k'aro lado kwance yayi fitsari gurin sai zarni yake babu me gyarawa suka had'a idanu tayi mai murmushi tare da k'arasawa gurinshi tana janyo tuwan da tagani wanda ko alamar ta6awa ba'a yi ba tace.

"Baffa bata baka abinci ba ko?" Ta fad'a tana shirin gutsurowa tare da kaiwa bakin shi yayi saurin bud'ewa sabida dama yinwa yake ji amma babu me bashi, yana ci yana jin kaunar ta na k'ara shigar shi, sai dai yana mamakin yadda yaga duk k'ankantar ta amma shigen surutu da iya sannan yadda zata yi komai, ta dad'e a gidan kafin ta koma gida, sai da ta dad'e a gurin bisjiyar kukan nan kafin ta shi ga ciki har lokacin babu wanda ya farka ta lalla6a tsakiyar su ta kwanta.....,

*{{ }}*

*INDIAN NEW DELHI*... All cikin university d'in cike take da al'umma kowa ka gani da abunda yake yi sannan babu ruwan wani da shiga harkar wani a cikin masu fitowa daga cikin wani katafaran hall harda Ma'aruf yafito hannunshi rik'e da brief case kai da ka ganshi kasan yana d'aya daga cikin wad'anda suka kwaso gajiya, tafiya yake a hankali amma shi a hakan mugun sauri yake, sai dai kai da kagan shi zaka ce ko baya san taka k'asa ne. Da d'an gudu budurwar ta k'arasa inda yake tare da sakar mata murmushi, kallonta yayi cikin takaici dayan baya buqatar komai yanzu banda ya kwanta gashi ita kuma zata uzzara mai, cikin tsuke fuska yace.

"Please n please Aisha kinga yanzun na fito daga lecture so ki barni naje na huta karki sa raina ya 6aci." Ma'aruf ya fad'a yana kallon cikin idanunta, kasa musa mai tayi sabida wani irin kwarjinin shi take ji hakan yasa yan zuma matsawa tayi ya wuce tabi bayan shi da kallo cikin tsananin so da begenshi har ya tari texi ya shiga tana tsaye.

Aisha budurwace kyakyawa gata da kamun kai, ba 'yar kowa bace hasalima da shocolaship tazo university d'in. Tunda idanuwanta suka dira akan na Ma'aruf taji duk duniya babu wanda take so bayan shi, da ta ganshi zata je inda yake wai ko zai kulata amma ina tayi hakan yafi sau d'ari hakan yasa duk tsananin kunyarta sai da ta tunkare shi akan suyi friendship amma kullum da uzurin da zai kawo mata duk da irin nacin da take mai.

Ma'aruf na komawa hotel d'in da yake brief case nashi ya ajiye kafin ya cire kaya ya shiga bathroom, wanka yayi sannan yayi alwala ya fito, pray mat ya shimfid'a yasan ya jallabiya coffee color ya hau yayi sallan asar, sai da ya idar sannan yayi shafe-shafen shi lokacin aka yi nooking door d'in ya bud'e ya kar6i odern abincin da yayi, dawowa yayi ya zauna a kan pray mat d'in yafara cin abincin tare da kunna t.v yana kallo. Sai da ya kammala komai sannan ya koma kan bed, laptop ya kunna ya fara laluban focal person  d'inshi dan yana son yaji karin bayani akan gwajin da suka yiwa lado.....

*{{ }}*

Yanzu kam baki d'aya al'ammuran hafsat k'arama ya fara bamawa kowa tsoro kasan cewar duk wanda yayi wani abun a gidan sai ta tona mai asiri, har wannan lokacin iyalan gidan nan babu wanda ko da wasa ya ta6a d'aukarta yara sa'aninta da wad'anda aka haifa bayanta duk basa kulata, jin dad'in ta kawai taje jikin bishiyan kuka ta zauna anan zaka ga farin ciki da nisha d'inta.

Zaune take yan zuma jikin kukar hannunta rik'e da wani kara karami sai kallonshi take tana dariya gashi daga ita sai pant yayi dukun-dukun da jirwayen fitsari hancinta duk majina ta bushe, Ard'o ne yazo wucewa da yaron shi a kafad'ar shi sai mika mata hannu yake Ard'o na bigiwa wai baxa shiba. "Ayd'o yana wasa ka bashi ni muyi taye."

Hafsat k'arama ta fad'a tana kallon Ard'o ya wurga mata harara "ke ki raba kanki da iyalina idan ba haka ba kaniyar ki zanci." Cewar Ard'o yana gyara wa Tanimu d'anshi rikon da yayi mai ta kuma kallon shi idanunta jawur kamar taruwar jini tace.

"Iya julai (zulai) matar Ard'o tana shama hira (fura) daka iteye (ajiye) a taki (d'aki)..." Numafar gidan Ard'o yayi yana shiga rumfar shi ya hangi zulai akan nono da furar daya ajiye yace sai dare zasu sha.

"Zulai *!* ya fad'a yana zaro idanuwa tare da ajiye Tanimu a kasa ya k'asa ciki yana kare mata kallo jikin ta sai rawa yake yau asirinta ya tuno tana goge baki Ard'o yace "daman kekike shanye duk abinda na kawo gidan ga amma kike cemin awaki ne ke shigowa ciki? Yau dai k'arama ta tona miki asiri kuma zan d'auki mataki akanki kinsan halina..."

Yana fita tayi kwafa tare da yin alwashin cin kaniyar hafsatu karama tunda ta tonata bayan shekara da shekaru babu wanda ya sani. Ita kuwa Umma Hafsatu har ta dena damuwa da halin da Hafsat k'arama ke yi dan idan ta hanata tonan sililin ma kamar k'ara zuga ta ake yi......










*FEEDOHM*💞
&
*HAJJA CE*👈
[7:31PM, 11/26/2017] 💧💧 Feedohm💞: 💧💧 *ABUNDA KE BOY'E……*
        《Almost True Life Story》

                   🍁🍁
                      💧

© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


        *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*
&
*_K.A.S Precious Hajja ce*👈


*SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《Ummana》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
 *Da dukkan masu suna HAFSAT dake duniyar mu*


        Page *21-22*

Hutun da yazo ne kwana biyu wanda sati biyu kawai zai yi yasa shi shiryawa dan komawa katsina, cikin shirin shi ya fito na blue jeans da white d'in t.shit hannun shi d'aure da whech mai ratsin color blue a jiki sai cover shoe white da siririn glass a fuskar shi yayi hanyar side d'in Madre.

"Ahh Ma'aruf yau kuma sai ina? Cewar Abba dake kokarin fita suka had'u a k'ofar parlorn. Kallon shi Ma'aruf yayi tare da yin k'asa da idanu yana sosa cikin dumbujejan lallausan gashin kanshi yace "Abba zan shiga katsina ne ina son nayi solving problems na wannan men d'in, so yau zan shiga gobe ko jiba zan dawo."

Abba yayi murmushin jin dad'i tare da cewa "To my son Allah yayi jagora ya kuma baka nasara." Ma'aruf yace "amin abba na gode sai na dawo." Daga haka suka yi sallama abba ya fita shi kuma ya k'arasa gurin Madre ta bashi breakfast yaci sannan suka yi sallama yayi mata fatan alheri yashiga mota drive yaja wannan karan ma basu yi sallama da Sumayya ba tana bacci ya tafi.

Yana sauka aka kuma had'ashi da wata sabuwar guider d'in, ta wannan karan tantiriya ce idanunta a soye suke sai dai kuma suna had'a idanu taji tana wani mugun tsoran shi ba shiri ta koma normal a matsayin na guard. Focal parson d'insa ne ya karaso sannan suka shiga mota suka wuce kauyan gwadabniya.


*{{ }}*    *{{ }}*

Yauma kamar wancan karan mutanan kyauyan suka dinga gudu tamkar zunga zakina, suna karasawa kofar gidan malan lado kundum ta fito da sauri tare da yank'are baki tana kiran Mai-tafasa.

"Wallahi kedai kam kundum kin shiga uku sauran ki kirss ki lalace, aikin banza ke badai ajiki da bakin alheri ba sai akan su Hafsatuwalle, aikin banza ai nasan dama yaune ake d'amrawa lauratu aure amma dan tsohon muna hirci kinzo zaki min gulma da....." Bakinta ya mutu lokacin da taga shigowar su Ma'aruf cikin gidan.

Direct cikin d'akin da Ard'o yake kwance suka shiga Ma'aruf sai faman toshe hanci yake sabida tsananin d'oyi, wari da hamami dake tashi a gidan, da kyar ya iya tsayawa a gurin lado yana mai gwaje-gwaje duk da anyi dama amma anga cutar AFP d'in sai dai rashin yin rigakafin yasanya yayi haka sannan kuma ba ita kad'ai ce tasa mai wannan larurar ba domin da itace zai iya moruwa da wani sashe na jikin shi amma wannan duk jikin shi babu mamora. "Mai kau Allah yasa dai lado na zai warke?

Cewar mai-tafasa tana dashare mai wawulan bakinta wanda yayi jawur gashi gaban ba hakura, banza yayi mata tare da bada wani magani focal person d'in ya d'ago lado ya bashi yasha sannan suka fito dan zuwa gidan mai unguwa sumai karin bayani.


*{{ }}*

Tararwa suka yi an gama d'aurin auren lauratu da sallau akan sadakin akuyar da sallau ya bada, karasawa suka yi gidan mai unguwa mutane suka biyo su mata da maza yara da manya ciki harda mutanan gidan su Hafsatuwalle, ita kad'ai ce bata fita ba kasan cewar ko taje da zagi da cin mutunci zata dawo. Carpet focal person ya fito dashi ya shimfid'awa Ma'aruf sannan mai unguwa ya zauna a shimfid'ar shi yana dasharewa Ma'aruf wangalelan bakin shi.

Banza yayi mai zai fara bayani sai ga lauratu ta karasa kusa dashi, "bature ashe zaka dawo garin mu? Ai munga  kaya sunyi kyau kuma ankasawa Hafsat tayi kyau Allah ya biya." Ajiyar zuciya ya sauke yana mamakin kafatanin 'yan garin "bature nima yau aka d'amra aure na kaga mijina can sallau." Muryar lauratu ta dakar mai cikin kunne, bin point d'in da tayi mai yayi da kallo har ya kai ga fuskar sallau yayi saurin rintsa idanuwan shi ya zura hannu ya Ciro 10k ya bata yace tayi hidima idanun mai unguwa akan kud'in yana son yasan yadda zai samu wani abun aciki.

*AFP* (Acute Flaccid Paralysis) ita ce ake cewa cutar shan'inna, sannan Likitoci sun ce a yankin kudu da Hamadar Sahara, mutum miliyan 12 zuwa 15 ne ke fama da cutar amosanin jini kuma kashi sittin cikin 100 suna Najeriya.
    ba a san haƙiƙanin yawan masu cutar amosanin jini ba, amma dai ƙwararru na cewa mutum miliyan ashirin zuwa miliyan ashirin da biyar ne ke fama da ita a duniya. Haka kuma duk shekara ana haifar mutum kimanin 2,400 masu wannan cutar.

Mafi akasarin inda ake samun yawan wannan cutar ta shan'inna shine *kauye*, cutar AFP na samuwa ne ta hanyar kazanta, rashin tsafta sune suke kawota, kuma tana samuwa ta kananan yara daga shekara 1 zuwa shekara 5. Malan lado yana d'aya daga cikin wad'anda ke da cutar sai dai rashin kulawa da rashin yadda da rigakafi da kauyan suka yi shine ya janyo mishi samun matsala a cikin jikin shi, wani lokacin idan ciwon ya motsa jikin shi babu inda yake mai aiki ko kuma yayi ta cewa a matsamai jiki sabida yadda yake ji a haka har..." Ma'aruf ya zaro idanuwa kirjinshi na dukan uku-uku ganin wata hallita tazo ta zauna akan cinyar shi sai wangale mai hakura take yi tamkar wata aljana. "Allahumma ajirni filmusibati fakalufli min khairu minha."

Ita kawai Ma'aruf ke fad'a a fili, ganin haka ne yasa guard d'inshi saurin zuwa dan ta d'auke ta sai taga idanuwan yarinyar sun koma wani irin abu tayi saurin matsawa baya tamkar wadda aka kafe ta tsaya. Masifa 'yan garin suka fara masifa ita kuwa Hafsat k'arama ta juya tana kallon Ma'aruf wanda ke zaune cikin tashin hankali sauran kiris ya saki fitsari yajiyo muryar mai unguwa na cewa.

"Ke shegiya k'arama kin tashi daka kan bakona ko sai na ham6are ki ja'irar yarinya fitinanniya...? Ya fad'a yana kokarin tashi yaji ya kasa, shi kam Ma'aruf daya tambatar da cewar mutum ce sai ya dawo cikin mode d'inshi amma duk da haka kirjinshi be dena bugawa ba ya kalleta yana kokarin  mikar da ita yaji tana shafa mai sajen da ya kewaye fuskar shi ya lumshe idanuwa zuciyar shi na shirin fitowa waje.... "K'arama zo tai gida gurin Umma min barta ita d'ai." Lauratu ta fad'a tana karasawa gurin tare da kallon Ma'aruf tace "bature Hafsat ce wadda ka siyawa kaya shekarun baya..." Tayi saurin jan hannuta shi kuma jin sunan yasa shi saurin bud'e ido........








*FEEDOHM*💞
&
*HAJJA CE*👈
[10:31PM, 11/28/2017] 💧💧 Feedohm💞: 💧💧 *ABUNDA KE BOY'E……*
        《Almost True Life Story》

                   🍁🍁
                      💧

© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


        *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*
   *&*
*_K.A.S Precious HAJJA CE👈_*

*SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《Ummana》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
 *Da dukkan masu suna HAFSAT dake duniyarmu*



     Page *23-24*



*D*a sauri ya mika mata hannu yana kiran "Common ……"

  K'arama tayi saurin fincike hannunta daga Lauratun ta dawo tare da zama saman cinyarshi ta zuba mashi manyan Idanunta !Kallonta kawae yake, yarinya mai kyau amma tayi duk'u duk'u da ita ……Idan baka kai zuciya nesa ba sae ka rantse ruwa bai tab'a hawa jikinta ba……

  "Yaro Ummana tace idan yaya Lauratu tayi aure dakinta zan koma……"Maganar da ta doki kunnenshi kenan yayi saurin maido natsuwarshi ……

 A Sanyaye yace "Ko……"

  Mai'unguwa yace "K'arama da k'warank'watsa na mike sae na ci Ubanki idan baki d'aga man bak'o ba……"


 Hararanshi tayi k'asa k'asa tana turo baki tace "Balan Sauka in ba! b'arawon masara……"

 
   "Uban Waye b'arawon "Ya fada a harzuke sannan yace "Kai bawale je kace Uwar wanga diya ta sameni gida idan rana ta take……"

  Ma'aruf ya kalli guard dinshi a raunane don har ga Allah ya gaji da zaman K'arama a jikinshi yace "Dauk'e ta zan tashi……" kafin ya rufe baki ta sakar mashi fitsari a jiki da sauri ya runtse ido zuciyarshi kamar ta fito dan takaici

  Zaro Ido tayi tana fadin "Sir wallahi baran iya taba ta ba ji kamar wata Vampire……"

  Lauratu ta matso a sanyaye ta kama ta da kyar suka shiga gidan tana turje turje ……

   A hankali ya mike ba tare da yace komae ba ya bude mota ya fito da robar swan ya fara tsiyayawa inda ta mashi fitsarin !Gashi duk inda ta taba a jikinshi kamar an debi bakin tukunya a shafa a gurin !tsaki ya saki lokaci guda ya shige motar yana kakkab'e jikinshi……Mai'unguwa ya rakashi ya rufe mashi motar sannan guard dinshi ta shiga suka tafi ……Suna tafiya mai unguwa ya fada gidansu yana kiran "Ke Lauratu fito"

  Cikin sauri ta fito ta tsaya gabanshi ta sadda kai a kasa don ta tabbata ba abun kirki ya kawoshi ba……Gulmammun matan gidansu da ba'a kira ba suma suka fito sukayi cirko cirko tsarkar gida suna jiran su ji ta inda zai fara ci mata mutunci'

  Bata fuska yayi yana hura hanci yace "Ina kudin da bak'ona ya baki……?

  Kanta na K'asa tace "Suna a daki na aje! idan Umma ta gama Sallah zan gwada mata "

Hura hanci ya kuma yana fadin "Rabasu Uku ki bani kashi biyu……!

  Da Sauri ta kalleshi take idanunta suka ciko da kwallah tace "Dan Allah mai ungua ka rufa man asiri ka bar kud'in dan Allah! wallahi ko langa Ummana bata sayar man ba da za'a ba uwar mijina!Yan kudin da muka tara kwanaki an sacesu tun dazu ummana ke kuka bata da abunda zata kai man a daki !Dan Allah ka rufa mana asiri tunda Allah yaji k'anmu mun samu !Wallahi idan bamu sayi komae ba Gori zamu sha da cin mutunci har ya'ya' da jikoki……"

  Banzan kallo ya watsa mata yana fadin "Bansan Shashanci banza !idan da bai baki kudin ba ya zakuyi!Ni mai unguwa nace kije ki raba kudi uku ki kawon kaso biyu idan kuma kika kara magana da k'warank'wasa duka zan karbe "

  Jummai ta tabe baki cike da bakinciki tace "Wallahi kama yi masu arziki da baka amshe duka ba Yo aikin me ta mashi da zai bata kud'i……!

  Laminde ta dauka da fadin "Yo Banda ma kana adalin Mai unguwa taya zaka bata kaso daya ka dauki biyu bayan gurinka yazo! aikin uban me ta mashi……?

 Washe baki yayi yana fadin "Kin kuma yi Gaskia Laminde ……"

   Lauratu ta fito rike da kudin a hannunta ta mika mashi Dubu Shidda ta dauki Hudu  tana hawaye …… kirgawa yayi yana fadin "Dubu Shidda kenan !ke nawa ne a hannunki?

  A Hankali tace "Dubu Hudu ne"

Bahaggun salati suka dauka suna fadin "Amma dae Lauratu anyi munafuka!Ina laifin ki dauki dubu uku tunda uku yace ki raba !wato mai unguwa zaki munafunta ko ?

  Girgiza kai tayi tana kokarin danne kukanta tana fadin "Wallahi a'a canji zan samo na cika mashi jikka uku da murtala……"

   Jummai tace "Uwar canji zaki samo bayan kin lahe kudi a hannunki !an dae ji kunya har mai unguwa ba'a raga mawa ba……"

  Warce kudin yayi daga hannunta yana fadin "Kin rasa duka wallahi munafuka kawae !ni wallahi na gaji da zamanku a wannan kauyen kun dauko zunubi kun hana mana bunkasar arziki……"

  "A Hayye……"Matan gidan suka dauko tare da kashewa suna dariya !Wata ta dauka "Mun ga abunda uwar taki zata hada maki zuwa gobe tunda an karbe wadannan masu bakin hali anyo abun kunya an dawo an tile mana anan …"

  K'arama dake tsaye bakin kofar bukka tana murda hannunta ta kallesu tare da kwashewa da dariya tana tabe baki "Wae abun kunya an tilele……"ta fada tana saukowa daga tudunkar ta nufo Lauratu dake kuka tace "Sae kiyi Hakuri Tunda shima ku'in (Kudin)nashi zubewa zasu har da na aljihunshi……"

  "To Mai bakin baki ……"Cewar Zulai matar Ardo tare da matsowa tana kallonta

  "Anya K'arama ba Mayya bace?Jummai ta amshe tana rike Hab'a

  "Idan itace ma yanzu zanyi maganinta wallahi!Jummai samman barkono da Tsakin kuka tare da kakkabin daudawa……"Zulai ta fada tare da fincikarta ta wulla wata tsohuwar Bukka dake kusa dasu……

  Da Sauri Lauratu ta rike Zulai tana fadin "Wallahi Inna Zulai ba Mayya bace dan Allah karki mata hayaki yarinya ce……"

 "Idan ba mayya bace ki bari a mata hayakin mana Tsohuwar munafuka" Jummai ta fada tare da mikawa Zulai Barkonon da tsakin kuka da Daudawa har da uban garwashin da ta debo a katuwar tukunya……

  Da Gudu Laure ta nufi Bukkarsu tana fadin "Umma dan Allah ki fito wallahi zasu kashe K'arama wae mayya ce"Turus tayi ganin Umman nasu tsaye tana lekensu ta wata yar kofar dake cikin bukkar tana kuka……

  Cikin kuka tace "Umma ki fito dan Girman Allah……"

  Girgiza mata kai tayi tare da rufe bakinta ta sulale gurin ta fashe da kuka mara sauti ……Sanin ko zata kwana a gurin Umman nasu bazata fita ba ya sata fita daga dakin da gudu ta nufi tsakar gida ……

  Tari ta fara da karfi tana dafe kirjinta jin azabar barkonon dake fitowa cikin Bukkar da suka rufe K'arama ……Bukkar ta nufa jin Tarin da K'arama keyi tana kokarin budewa amma Jummai ta kwalfa mata mari tare da hankadata gefe tana fadin " Yau *ADUNDA KE B'OYE* Ga wagga yarinya sae ya fito dan ubanki ……Kuma da k'warank'wasa ya tabbata mayyace sae mun hada wuta mun jefa Shegiya"

  Har Sae da Hayakin ya bar fitowa daga Bukkar sannan Zulai ta bude, lokaci guda ta waro ido tare da ja da baya tana fadin "Na ga Shegiyar yarinya !Wato dan ubanki carafke kike ko ……"ta fada hade da karasawa cikin dakin ta janyota tare da watsa mata mari tana fadin "Idan ke ba mayya bace to ke Shegiya ce kuwa!

  Kwace hannunta tayi tana wurga mata Harara ta K'asan ido tace "Kece Mayyan Julai……"

  Sannan tayi gaba ta barsu tana tsallenta har ta shige Bukkarsu ta fada saman cinyar Umman tana fadin "Na ci dad'i yau Ummanmu……"

   Kasa ce mata komae tayi sae rungumota da tayi tana kuka ……Ita kam K'arama bata ga abun kuka ba don ta haka ta ware idanu tana kallon Umman tata ko kyaftawa batayi……

  Lauratu kam bayan Zulai ta mareta bayan gida ta zagaya ta zauna tare da hade kai da guiwa tana kuka ……Dafata da akayi ne ya sata dagowa da sauri tana kallon Matashiyar yar fillon dake tsugunne gabanta ……
 
   Cikin Fara'a yar fillon ta janye hannunta daga jikin lauratun sannan ta janyo wata karamar jikka ta mika mata ……K'in karba tayi tana kallon Yar fillon cikin rashin sani don bata taba ganin mai ko kama da ita ba a yankinsu……

  "Ungo Lauratu……"Yar fillon ta fada tare da kamo hannunta ta daura mata jikkar ……Kafin ta bata amsa ta mike da sauri ta bar gurin……

  Kallon Jikkar Lauratu tayi a sanyaye sannan ta mike ta koma cikin gida har lokacin tana kuka mara sauti ……Ganin matan gidan ko wace ta kama harkar gabanta yasa ta shige bukkarsu da sauri……Ganin Umma kuka ya sata sulalewa a k'asa tare da yarda jikkar ta hau nata kuka ……Ita kam K'arama raba ido take ta kallansu……


《》《》《》《》

  Ma'aruf kam tunda suka shiga motar ya rufe idonshi gam ya kasa budewa K'arama yake hangowa lokacin da ta saka k'azamin hannunta ta shafi sajenshi !K'ara runtse idonshi yayi yana girgiza kai ……

  Driver ya kalleshi yace "Sir da matsala ne……?

  Girgiza mashi kai yayi a hankali yana ware hannunshi daga jikinshi……Guard din ta saki dariya cikin sigar jan hankali tace "Sir ya hadu da aljana ne……"

  "Haba dae……"Driver ya fada yana dariya a hankali……

  Dariya ta kuma yi tare da leko kanta tana kallon Ma'aruf din tace "Serious!Sir ka bude idonka mun bar garin sossae fa……"ta karashe maganar tana kashe murya……

  Duk abunda suke fada yana jinsu amma tsabar Aji irin nashi ya hanashi bude ido bara ya kula su ……

  Office dinsu suka yi parking lokacin Yan'mata ke ta dawowa daga aikin da suka fita ……

  Katuwar tabarma ce cikin barandar office din Focal Persons na wards tare da team volunteer da CCO da Facilitator ke zaune suna cin abinci hankalinsu kwance……

  Rab'a su yayi ya wuce ya zauna bisa kujeran dake gefe guda tare da rufe ido kamar yana ganin wani abun cuta……

  Gaidashi sukayi ya amsa masu ta hanyar daga masu hannu ba tare da ya bude idonshi ba ……

  Facilitator ya matsa yana fadin "You're welcome sir!Tun dazu Director ke jiranka
a ciki……!




*HAJJA CE👈*
  *&*
*FEEDOHM💞*
[10:33PM, 11/28/2017] 💧💧 Feedohm💞: 💧💧 *ABUNDA KE BOY'E……*
        《Almost True Life Story》

                   🍁🍁
                      💧

© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


        *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*
   *&*
*_K.A.S Precious HAJJA CE👈_*

*SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《Ummana》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
 *Da dukkan masu suna HAFSAT dake duniyarmu*



       Page *25-26*


Ba tare da ya bude ido ba yace "Ta fito nan……!
  Cikin kulawa facilitator din ya kalleshi yace "Da matsala ne Sir……?

  Kafin ya bada amsa Guard din tace "Oga da Matsala wallahi !wata aljanar yarinyace ta haye jikin Sir duk ta birkita mana shi……"

  A Fusace yace "A ina?

   Tabe baki tayi tana fadin "A Wannan karamin kauyen da ake samu mai AFP case dinnan fa……"

 "Ina Mai unguwar garin?Meye amfaninshi da za'abar yara suna zuwa kusa dashi?kema meye amfanin ki? sannan meye amfanin driver'n da aka hadaku dashi?Kin san waye shi……?ya karashe maganar cikin tsawa

  Jiki a sanyaye tace "Sorry oga wallahi yarinyar ce kamar Vampires ……"

 "Keep quite!wallahi wani abu ya sameshi ba katsina state ba dukka nigeria sae munyi Sharing tears !WHO Consultant ne shi……Kiraman driver yanzu ……"

  Bude ido yayi yana kallonsu sannan ya bude baki da kyar yana fadin "Am Ok……!

  Da Sauri Facilitator yace "Sorry Sir wallahi ban san wannan shashancin zai faru ba da dani aka je kauyen!

  Maida idonshi yayi ya rufe yana fadin "Is ok……

  Bala'i Facilitator din ya cigaba da yi shi kadae ita kanta Guard din tayi nadamar fada da tayi ……Sae da yayi mai isarshi sannan ya shiga ya kira Director din ……Sama sama suka cigaba da maganar sannan aka kawo mashi abinci amma yarda suka aje haka ya barshi har sae da lokacin meeting yayi sannan ya mike suka tafi ……

A Gurin meeting din ma sae da Facilitator ya fadawa Hakimi abunda ya faru ……Shi kanshi hakimin cewa yayi zai saka a kira mashi Mai unguwa Audun yaji dalilinshi na barin yara suna zuwa gurin bak'onsu har su tabashi……

Shi kam wanda akeyi donshi banza ya masu don bai ga abun tada jijiyoyin wuya ba!aciki bakin cikinshi d'aya kayanshi da ta b'ata tare da fitsarin da ta mashi a kaya, ga wani irin wari da yake ji yana yi duk idan ya rufe idonshi ……

【】

 Mai unguwa kam tunda ya karbi kudin ya soke aljihu ya kama dan kekenshi ya haye ya yanki daji yana y'ar wak'arshi a hankali ……Yayi nisa da tafiya ya hangi wata yar K'aramar yarinya tsaye gefen hanya tana kuka ……

  Sae da yaje gabanta sannan ya tsayar da keken da kyar yana kallonta yace "Na ci Gidanku !Banda iskanci sae yara su zo su tsaya tsakiyar hanya suna wa mutane kuka !Ina iyayenki……"

 Da Hannu yarinyar ta nuna mashi cikin daji har lokacin tana kuka !Tsaki yaja yana fadin "Ni k'warank'watsa ma ban taba ganin mai kalarku ba a cikin yankina ……dan biri "ya karashe maganar yana dariya sannan yace "Ke yarinya yaushe kuka dawo nan yankin?

 Da katuwar Murya tace "K'wanan mu biyar……"

Dariya ya saki yana fadin "Kam bala'i ka ji man yarinyar da Muryar k'arti !Ba mamaki wannan K'wababbar fuskar taki ita ta dace da wannan Hegiyar muryartaki……"Ya karashe maganar yana dariya……

  Kafe kekenshi yayi jikin hanyar Sannan yayi hanyar da ta nuna mashi yana nade katuwar rigarshi yace "Mu je ki gwada man iyayen naki naji shegen da ya basu damar zama a yankina ba tare da izini na ba……"

  Bata ce mashi komae ba tayi gaba ya bi bayanta sae surutai yake shi kadae……Tafiya sukayi mai nisan gaske amma da yake ya shirya rashin kirki bai lura da nisan ba!Wasu yan bukkoki suka iske a tsakiyar daji sannan ta shige bukkar da sauri ta barshi tsaye ……

 Wage baki yayi yana fadin "Owoo ni za'awa Shegantaka a barni tsaye? to yayi dai dai yarinya ba da ke zanyi ba yanzu da iyayenki zanyi !

  Daga Murya yayi yana fadin "Bai zama dole na maku sallama ba tunda ban san da zamanku a yanki na ba!Ina mai gidan fiton ka fada man wane Shege ya baka izinin zama k'asata ba tare da yarda ta ba……"

  Wani dattijo ya fito sanye da rawani irin na buzaye yana fadin "Marhaban wa ke kirana haka ……?

  "Mai ungua Audu ne……!ya fada yana mazurai

  "Maraba mai unguwa……"Tsohun ya fada yana matsowa

   "Ba wani maraba dattijo zuwa nayi naji wane she……"Maganar ta katse ganin bindi a bayan dattijon

    Girgiza kai tsohun yayi yana fadin "Ka ce mene Mai unguwa Audu?

  Mazari ya fara yana fadin "Na…ce rigim rigigim !na kuma cewa Bindi……"Kwasawa yayi da gudu yana nade babbar riga !gudun ya tsaya lokacin da wasu karnuka suka tare mashi gaba……Ihu ya saki yana sakin fitsari kafin ya canza hanya ya kara kwasa da gudu……

   Gudu ta dinga yi cikin dajin yana haki yayin da karnukan suka mara mashi baya suna wani irin Haushi ……Da kyar ya fito hanya! bai tsaya daukar kekenshi ba ya yanki hanyar Garinshi ……Sae da suka kusa shiga garin sannan karnukan suka daina binshi suka juya suka shige daji ……

  Kusa da gidanshi sukayi Karo da Mai tafasa ya ja numfashi ya tsaya yana fadin "Na Shiga Uku ni Audu wane irin mutane ne yau na gani……"

 Watsa mashi harara tayi tana fadin "Amma dae Mai unguwa Audu an tab'e !Me ya biyo maza da suke tafiya suna sakin fitsari a wando?

  "Ke Mai tafasa bana son ruwan tabbata nine na Tabe……"ya fada har lokacin yana haki

 Watsa hannu tayi tana fadin "Idan akwae wani Audu mai jikakken wando anan gurin to dashi nake !Bana son munafunci bani kudin Tafasa ta da ka ci jiya!……ta karashe maganar tare da wurga mashi hannu kusa da fuska

  Tsaki ya saki yana fadin "Don kina bina Muttala zaki shine zaki man tabbata……!ga dubu ki bani canjina kuma da k'warank'watsa ko motsi ba zakiyi ba sae kin bani canjina……"ya karashe maganar tare da lalubo aljihunshi ……

   Ido ya wurgu waje jin babu komai a aljihun sae kullin wani abu a leda ……Fiddon shi yayi da sauri yana jujjuyawa ganin Nono ne kindirmo a cikin ledar "Wa kuma ya bani nono……"Ya fada tare da maida hannunshi aljihu yana lalubar kudin amma wayam babu su ……

  A rude yake fadin "To ina na yarda kudinnan……"

  Juya mashi baya tayi tana d'age kallabinta ta fiddo keya tace "Koma ina ka yardasu Mai tafasa dai kudinta take bukata……"

  "Kinga wallahi Mai tafasa da kudin aljihuna……"Ya fada kamar yayi kuka……

  "Wallahi banda mutunci Audu ka fiddo man kudina yanzu !

  Da kyar ya lallabeta ta hakura ta tafi gida tana mita……sannan ya shiga gida kamar ya fasa ihu yana tunanin kila gurin gudu ya yarda kud'in kuma babu damar komawa ya duba ……Bai samu ya samu sauki ba sae da ya fitar da kwallah saboda bak'in cikin kud'in !Ranar duk wanda ya mashi magana a gidan zai sha zagine har na fitar hankali……ji yayi dama ya barwa Lauratun kudin bai karba ba……





*HAJJA CE👈*
  *&*
*FEEDOHM💞*
[6:42PM, 11/30/2017] 💧💧 Feedohm💞: 💧💧 *ABUNDA KE BOY'E……*
        《Almost True Life Story》

                   🍁🍁
                      💧

© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


        *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*
&
*_K.A.S Precious HAJJA CE*👈


*SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《Ummana》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
 *Da dukkan masu suna HAFSAT dake duniyar mu*


        Page *27-28*


   *M*ikewa k'arama tayi tabar musu d'akin ganin sai faman uban kuka suke yi, gurin mai unguwa ta koma ta tarar baya rumfar shi sannan ta koma gindin bishiyar kuka ta zauna sai dariya take tana faman surutu, duk wanda ya ganta sai ya tabbatar da cewar ta samu ta6in hankali ta yadda take kwasar dariya ba kakautawa....,

"Ard'o wallahi k'arama ba mutum bace dan mun tabbatar da hakan yau d'innan." Cewar laminde da taga shigowar Ard'o yayi saurin kallonta da mamaki yana kokarin ajiye sandar korar awakin shi yace.

"Laminde ban shaida zancen kiba, hito kiyi min hila-hila." Cewar Ard'o yana kallon rumfar su Umma hafsatu, laminde tace, "kur'anin Allah bari jummai tazo kaji karin bayani."

K'arama ce ta biyo Tanimu yana rarrafe yana dariya har ya karasa kusa da Ard'o cikin 6acin rai ya kalli k'arama tare da gallara mata harara yace, "dan kaniyar ki ban ce kar in kuma ganin ki da yarana ba? Ja'ira kawai fitinanniya marar tushe."

K'arama ta tura mai baki tana mai kunkuni har jummai ta fito daga makewayi (toilet) duk ruwa jikinta daga gani tana nufin wanka tayi amma duk wani gurin bema san an hallici ruwa ba ta karasa inda suke dama tun a ciki take jiyosu gulma na cinta ta fito tana cewa "Ard'o babu shakka yau mun tabbatar da cewar k'arama mayya ce dan munyi mata hayak'i karshe ma caraffke mukaga tanayi a ciki.."

Zaro idanu yayi cikin tsananin mamaki da tsoro yace "ta6 d'i jam *!* abinda ba zai yiwu ba kenan shine take son ta fara takan yaro na kenan...?"

"Ke Hafsatuwalle... *!* zo nan." Ard'o ya fad'a cikin d'aga murya, Umma ta fito bayan ta goge hawanta. "Ke kam wallahi hafsatu kin janyo mana bala'i, ko waye uban k'arama ya had'a jinsi da mayyu dan haka Mu bazamu yadda ba mun baki nan da sati biyu idan baki binciko mana uban k'arama ba wallahin Allah zaki gane kuran ki."

Kuka ta sanyi a gurin zuciyar ta na zafi k'iris ya rage ta kone kurmus a yadda take yi mata zafi da rad'ad'i. "Umma tashi Mu koma d'aki dan Allah.." Cewar lauratu da itama take sharar hawaye tamkar ba amarya ba haka suka koma cikin rumfar su.

Kusan awar su biyu sannan suka share hawayen su Umma ta kalli kud'in hannun lauratu tace "Laure wannan kuma daga ina?" Ta fad'a tana tsinkar zogalen da zata dafa tabawa lauratu a matsayinta na amarya me jiran tarewa anjima a d'akin ta.

"Umma wata fillo ce ta bani, ban santa ba kuma har tambayar ta nayi amma ta wuce bata ce min komai ba." Kar6ar kullin Umma tayi tana bud'ewa taga kud'i masu yawa wajan 22k duk an cure su guri guda. "Lauratu kud'ine... *!*" Umma ta fad'a hannuta na rawa idanunta a waje tana kallon lauratu, "ke nan kyauta ta bani? Amma ban santa ba hasalima ban ta6a ganin gilminta a yankin Mu ba."

K'arama ta shigo tana rik'e da d'ankwalinta a hannu ta kallesu duk sunyi zugum abin tausayi, karasawa tayi ta zauna ta kalli Umma tare da wangale bakin ta tace "Umma fillo ce ta bayar a siyawa ya laulatu (lauratu) kwanika shabida (sabida) su jummai kalltuyi (karsuyi) mata gori..."

"Naji k'arama amma waya gaya miki...?" Umma ta tambayeta k'arama tace "fillo ce Umma." Nan da nan suka yi murna tamkar su zuba ruwa su sha. Nan da nan kuwa Umma ta mik'e ba wanda ya sani rabar gidan harta je ta dawo babu wanda ya lura.

"Inno a fito da amarya Sallau ya gama komai." Cewar matan gidan wad'anda suka fito kwansu da kwarkwatar su suna jiran a fito da lauratu aga kwa-kwaf.

Inno dake cikin rumfarta tana ji tayi shiru dan ita kanta kunya take ji, ya zata fita guri ace anyiwa jikarta aure ba ko cukali, gara tayi zaman ta dan baxata fita ba suje can suyi tayi babu abin da ya shalleta. Mutanan gidan kuwa sai munafirci suke suna kus-kus, cikin d'aki kuwa Umma ce ke yiwa lauratu nasiha sannan kwanikan da ta kar6o gidan jauro guda biyar ta ajiye su guri guda sai guru daya siyar mata 5k shima duk yaci duniyar shi sabida kayan matar shine da ta rasu kuma dama ba a kauyan take ba irin filanin nan ne masu tafiye-tafiye shi yasa shi kuma yake siyar da kayan d'akin nata.

"Ahayyeeee ayyrrrrrrrri.... *!*" matan gidan suka d'auki shewa gaba d'ayan su harda mazajen su ganin Umma ta fito da lauratu cikin lullu6inta, a haka ita da k'arama suka shiga d'akin da yake a matsayin na lauratu Umma ta zaunar da ita a wajan da taga an ajiye tabarma sannan ta koma rumfarta ta d'akko garun da langunan ta kuma komawa inda lauratu take, ganin ta shigar da kaya yasa mutanen gidan bin ta suna mamaki har ta shimfid'a mata garun tare da ajiye mata sauran kwanukan ta ra6a mutanan ta wuce tana sharar hawaye.

"Ahayye nanayeee Tambai ku ganemin a ina suka samu wanga kaya..?" Jummai ta fad'a tana rik'e da ha6a cikin tsananin mamaki, maganganun sune yasa inno fitowa itama ta leka nan taga lauratu zauna gefe kuma langunan tane inno tayi d'akin Umma da sauri cikin tashin hankali.

Karo na farko kenan da inno ta ta6a shiga cikin d'akin Umma, karasawa tayi tana tambayar ta "Hafsatuwalle ince dai na sahun 6arawo kuka fara ba..? Ina kunka samu wanan kaya haka nayan baku ajeba bare ku bayar da ajiya." Umma ta kalli inno tana mamakin yadda mahaifiyar ta tak'i ta cikin sanyin jiki tace "inno daga Allah ne, Allah ne ya bamu."

"Karya kike Hafsatu ai komai akwai sila ki sanar min kamin ranki ya kuma 6aci." Ta fad'a cikin d'aga murya, shigowar k'arama ne yasa inno juyawa tana kallonta k'arama tace "Inno gashiya (gaskiya) Umma na ta gaya miki domin fillo ce ta bawa ya laulatu tashi Umma na ta shiyo mata kayan..."

Tunda k'arama tayi magana inno taji ta kasa musawa gashi ranta na son furta abu amma bakinta ya gaza fad'a a haka tabar d'akin tana mamakin alamarin. "Ard'o da laminde sune suka 6oye tukunyan baba shallau.." Suka jiyo muryar k'arama na fad'a a tsakar gida, da gudu laminde ta bita tana zagi wai tayi mata sharri kumma haka ne sun 6oye dan azo ana cigiya ace Umma ce ta d'auke.

Ba jimawa bayan kowa ya gama gulmar shi sallau ya shiga ciki murna tamkar an bashi sarautar garin, koda ya shiga d'akin dashare baki yayi yana murna, shi duk be damu da komai ba illah kawai ya yanshi da lauratu dan ba karamin sonta yake yi ba daga nan kuma......


*{{ }}      {{ }}*

     *"M*ai-tafasa wallahi idan baki rabu dani ba zan bar  miki gidan, haba mata sai jarabar tsiya shi yasa bana son zuwa gidan nan sabida masifarki." Cewar mai unguwa cikin 6acin rai, ga bak'in cikin zubewar  kud'in shi gashi ita kuma ta sashi a gaba tana sakar mai magana.

"Yoo ni ina ruwana cewa nayi ka dinga fita da kud'i ko ina? Sabida baka yadda da kowa ba toh kur'anin Allah sai ka biyani kud'ina ahe..." Mai-tafasa ta fad'a tana kokarin shiga d'akin da lado yake ciki a kwance gwanin ban tausayi duk yayi kashi d'akin sai d'oyi yake yi tamkar bayin da ba'a wankewa.

Ko takan kashin bata yi ba nan ta ajiye mai farau-farau d'in data yi tasa kai ta fita, tana fita k'arama ta shiga ta d'ayar kofar ita ce ta gyara mai jikin shi sannan ta bashi farau-farau din tare da bashi labarin auran lauratu har hawaye yayi yana ta faman jin-jina kanshi abin tausayi.

Ta dad'e a gurin shi sannan tafi gida lokacin lauratu na d'akinta har lokacin bata fito ba sabida tsananin kunya da take ki, sallau ne keyin komai hakan ya Kara tabbatarwa da mutanan gidan komai ya wakana....









*FEEDOHM*💞
&
*HAJJA CE*👈
[6:42PM, 11/30/2017] 💧💧 Feedohm💞: 💧💧 *ABUNDA KE BOY'E……*
        《Almost True Life Story》

                   🍁🍁
                      💧

© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


        *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*
&
*_K.A.S Precious HAJJA CE*👈


*SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《Ummana》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
 *Da dukkan masu suna HAFSAT dake duniyar mu*


        Page *29-30*

     *B*ayan Ma'aruf ya kammala karatun shi ya dawo Nigeria Aisha budurwar shi dake tsananin son shi da kyar ya samu ta rabu da shi lokacin har kuka tayi da yace mata anyi mishi baiko da wata tayi kuka sosai dan ba karamin so take mai ba shima lokacin yaji tsananin tausayin ta amma ba yadda zai yi dole yasa ya gaya mata gaskiyar lamari.

Zaune yake a parlorn Madre yana karanta wata jarida Sumayya ta fito, tana ganin shi ta koma room d'inta tare da kara turare a jikin ta kasan cewar tasan yana son kamshi. Parlorn ta koma ta zauna bayan ta gaidashi ya amsa tamkar baya so, kafin ya d'ago ya kalleta suka had'a idanu guri d'aya yace.

"What are you looking for?" Ya fad'a bayan ya d'aure fuska Sumayya tayi murmushi tare da gyara zama ganin yana son magana tace "Yaya Ma'aruf naji ka shiru baka min zancen yadda bikin Mu zai kasan ceba kayi shiru..."

Jaridar hannun shi ya ajiye tare da kallonta, "please come close to me zan gaya miki..." Da sauri ta mik'e ta k'arasa kusa da shi tana mamakin jin cewar yace ta dawo kusa dashi, shi kuwa tun sanda ta shigo parlorn kamshin turaran ta ya bugar mai hanci duk sai yaji ya diririce kaunar ya ta6a ta ya shigar mai zuciya sa bida khamran ta rikita shi.

"Kin gane ko Sumy *!*, bana bukatar yin wasu bidi'u just kawai a yi lalle ranar d'aurin aure sai ayi walima kawai, albarkar auren muke so ba wani abu ba...."

Turo baki tayi cikin shagwa6a, hannunta na cikin nashi ji yake tamkar ya rungometa amma bazai iya ba gudun kar ya janwowa kanshi fitina, abinku da lafiyayye giredin namiji mai ishashishiyar lafiya. "Haba Yaya Ma'aruf ko dinner ma baza muyi ba, please dan Allah mana sai kace ni dakai ba wayayyu ba...?"

Mteww... *!*, yaja tsaki cikin jin haushi a hankali ya zame hannun shi dake cikin nata ya d'auki jaridar shi daya ajiye yace "ok fine, kije kuyi but ni dai baza ku ganni a wajan ba that's all..."

"Yaya Ma'aruf why zaka yi mana haka..?" Sumayya ta fad'a kamar zata yi kuka, Madre ce ta fito hannunta d'auke da memo da biro ta k'arasa parlorn ganin su tare yasa ta saki murmushi tace,

"Yauwa gara da na ganku tare Ma'aruf my son, ina so naji wane color kake so na punitures d'in ka?" Madre ta fad'a bayan ta zauna cikin d'aya daga kujerun.

Cikin rashin son maganar shi ya kalli Madre tare da miskilalliyar fuskar shi yace "Madre I don't have a choice, so choose me any colorful..." Murmushi tayi dan tasan color d'inshi ta koma kan Sumayya dake ta faman cono baki daga gani tana cikin fitina Madre tace...,

"Ya haka kuma Sumayya..? Waya ta6a minke haka da safen nan? Sumayya ta juya tana nuna mata Yaya Ma'aruf da hannu fuskarta a shagwa6e. "Sorry baby kinji rabu dashi zo ki gaya min abinda yayi miki...."

Zama tayi kusa da Madre tace "kinji shi wai baza muyi kowanne event ba, ko zamu yi shi bazai je gurin ba...." Madre ta zaro ido tana kallon Ma'aruf cikin mamakin shi tace "wai Ma'aruf wane irin mutum ne kai ah..? To za'a yi koma sai kaje komai kaji na gaya maka..."

"Okk Madre fine, a tuna nina albarkar auran ake so, amma tunda kince haka zanje..." Yana fad'a ya bar parlorn cikin jin haushi, side d'in shi ya wuce ya d'auki laptop d'inshi yana wani research......


*{{ }}       {{ }}      {{ }}*

      Karasawa suka yi cikin gwadabniya har cikin d'akin da lado ke kwance, Ma'aruf ya kalli side d'in da wani babban malami yaje wanda suka zo tare yace "bismilah malan kalla..." Malan Kalla ya matsa kusa da lado dake kwance yana binsu da ido, wata jaka ya bud'e gaba d'aya d'akin ya kaure da kamshin almuski nan da nan lado ya fara zaro idanuwa yana kokarin yin motsi da 6arin jikin shi d'aya.

Kura mai idanu Ma'arf yayi yana nazartar wani abu daga jikin shi, malan kalla ya fito da garin ganyen magarya da jikakiyar kanwa ya fara watsa wa a gurin da lado ke kwance. Ayatulkursiyu yace su karanta baki d'ayan su mutanan gurin su focal parson, guard, Ma'aruf, mai unguwa da makocin su malan sahabi kowa sai mamul-mamul yake da baki idan ka d'auke malan kalla Ma'aruf da focal parson sune kawai suke yinta dai-dai, nan da nan ana watsa mai ruwan kanwa da ganyen magarya lado ya fara wani irin kuka kirjin shi na d'agawa, Ma'aruf ya gazgata zargin shi na cewar asiri aka yiwa lado.

Wata irin murya suka ji gaba d'aya ta kaure cikin d'akin tamkar zata tsaga bango, kallon lado malan kalla yayi tare da cewa "wace ce ke..? Me kike yi ajikin bawan Allah kike wahalar dashi tsawon shekaru..?" Siiiiiiiiii..... *!*, suka ji yana fitowa daga bakin lado malan kalla ya shafa mai ruwan kanwa sai aljanar ta fara magana a fusace.

"Ku-ku-kun takura mana fa... *!* kai.., ta nuna Ma'aruf da yatsan lado tace "ka takurawa rayuwar mu, ka hanamu sukunin da muka dad'e muna yi, ina ruwanka damu da zaka tahu mana da kalla...... *!*?" Ma'aruf yayi murmushi cikin nuna rashin tsoro duk da bugun da zuciyar shi ke mishi yace.

"An so what..?" Ya fad'a tare da mai da kallon shi gurin malan yace "continue malan daga inda ka tsaya..." Ayoyi malan kalla ya dinga kwararowa aljanar tana ta magana kafin ogan yayi shima cikin zunduma uban zagi dama bama gujene malan kalla yace.

"Ina jin ku me ya faru..?" Ifiritu yayi magana a kausashe yace "turo mu aka yi kuma mun samu gurin zama dan munyi katon gini a jikin shi..." "Waya turoku jikin shi..." Hhhhhhhh.... *!* ifiritu yayi wata mahaukaciyar dariya tare da cewa "babu ruwanka."

Karatu malan kalla ya cigaba dayi su kuma suna ihu suna cewa yayi hakuri zasu fita kuma zasu fad'a amma yak'i denawa lokacin duk mutanan gurin sun shiga cikin rud'ani sai da ya kusa konasu da ayar Allah sannan ya watsa musu ruwan kanwa yace toh muna ji waya turo ku?" Ifiritu a wahale tamkar d'an giya yace "Hansai ce matar mai-unguwa ta biyu, ta turo mu ne ganin suna zaune lahiya da Hafsatuwalle sannan mai-unguwa naji dashi hakan yasa ta turo mu muka shige shi karku konamu muna da yawa muda iyalanmu...."

"Kanbala'i! Aradun Allah bazan yadda wato daman Hansai ce ke son lahanta min lado...?" Cewar Mai-tafasa dake bakin kafa, "tallahi banga me rabani da Hansai ba a garin nan daman tuntuni naga take takenta kundum, buwale, Asibi, baraka, lanto kai duk mutanan garin nan kuzo kuji min Hansai ta cuce ni ita ce ta kwantar da lado..."

Kafin kace me sun cika gidan yaran su da manya, nan mai-tafasa ta kara narka wani bala'in su lanto suna zugata haushi da takaici yasa Ma'aruf ya fito yana kallon su tamkar yayi amai sabida tsamin da ke tashi a jikin su yace, "shut up *!*, duk da basu gane me yake cewa ba amma sunga yayi tsawa sannan fuskar shi a murtuke yasa suka yi shiru yace su fita daga gidan su basu guri, sim-sim suka fita harda Mai-tafasa sannan yayi tsaki ya koma cikin d'akin malan kalla nata karatun alkur'ani su kuma sun zuba musu idanu, karasawa yayi suka ci gaba tare har kusan tsawan awanni biyar kafin sukayi nasarar kona su baki d'aya.

Waige-waige lado ya fara yi yana kiran Hafsatu, ganin bata fito ba yasa ya kalli mutanan yaga Mai-unguwa yace "Baffa malan ina Hafsatu na..?" Sai ga mai-unguwa na hawayen murna yau yaji muryar lado daya dad'e beji ba. "Tashi mugani.." Ma'aruf ya fad'a yana kallon lado cikin ido, "ba zan iya ba rankashi dad'e..." Lado ya fad'a yana zubar da hawaye Ma'aruf yasa focal parson ya tatta6a shi sai yaga 6arin jikin shi na hago baya aiki nan yayi musu bayani daman hakan zata faru kasan cewar yana da matsalar AFP sannan kwanciyar da ya dad'e guri guda yasa hakan yayi tasiri yanzu haka lado sai dai a samo mai weal chair da keke ya dinga amfani dasu, sun d'an jima kafin suka bar gurin su Ma'aruf suka koma state dan sanar dasu abunda ke akwai.......,













*FEEDOHM*💞
&
*HAJJA CE*👈
[6:58AM, 12/1/2017] 💧💧 Feedohm💞: 𹰠💧💧 *ABUNDA KE BOY'E……*
        《Almost True Life Story》

                   🍁🍁
                      💧

© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


        *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*
   *&*
*_K.A.S Precious HAJJA CE👈_*

*SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《Ummana》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
 *Da dukkan masu suna HAFSAT dake duniyarmu*


 
         Page *29-30*


   K'arama kam Tana ganin Sallau ya fito ta fad'a dakin da gudunta ta Samu lauratu rakub'e jikin bango sae sunne sunnen kai take ……Kusa da ita ta rab'a ta zauna tana leken fuskarta tare da dashire dan k'aramin bakinta tana fadin "Yaya Laulatu yau ba'a d'akin Ummanmu kika kwana ba ko?

 K'ara sunne kai tayi kamar tana magana da wata babbar mace ba tare da tace komae ba

 "Yaya Laularatu bakin ki ke ciwo ne?K'arama ta tambaya ganin tak'i mata magana……

  Cike da kunya ta girgiza wa K'arama kai ita ala dole kunyarta take ji……
 Tabe Baki K'aramar tayi tana kallon Sallau da ya shigo dak'in rike da katuwar langa a hannunshi tace "Su Malan Sallau angon Yaya Laularatu!Uhm ango da amarya manya !Bara dai na tashi Nasan Ummana na can tana jirana……"

 Sallau d'in ma sunne kai yayi k'asa yana satar kallon Lauratu da murmushi kwance a fuskarshi!Sannan ya aje langar hannunshi ya juya da sauri kafin K'aramar ta fita ya bar dakin ……

 K'arama na ganin ya aje langa gaban Lauratu ta kuma k'yalla ido ta ga naman zabbine a ciki an dafa su da barkono ta dawo ta zauna tare da janyo langar sossae gabanta tana fad'in "Yaya Laulatu ki sako hannu ki ci idan kuma baki ci ni na cinye maki bs ruwana ……"

  Shirun da K'arama ta ji ne ya sata saka hannu ta fara cin abunta hankali kwance tana lashe hannu har sae da ta ci kusan rabi sannan ta debi wani a hannu ta mike tana fadin "Idan bara ki ci ba ki aje man anjima zan dawo na karasa cinye abuna ………" Har ta fita Lauratun bata dago kai ba wae kunyar K'aramar take ji ……Ita kam wadda akeyi dominta bama tasan me take nufi ba !ta dai fita dakin da namanta a hannu ……

  Munafukan gidan suka dauki salati tare da taba hannu suna kallonta rike da nama a hannu !Kukan kura Zulai tayi ta warce naman daga hannunta tana fadin "Amma K'arama anyi shegiyar yarinya yanzu naman da ko ni da na dafa ban ci shi ba shine kika shiga dak'i ki cinye shi dan kina karamar mayya ko ……"

 Turo baki tayi tana murguda baki kasa kasa kafin ta zagayesu ta wuce ba tare da tace komae ba !Har sae da ta kusa fita bakin kofar gidan sannan ta juyo tana kallon su tace "Allah ya wa'e (watse)maki albarka Julai……"Ta fice gidan da gudun tsiya ……

  Zulai ta d'aga kafa zata bita jummai ta riketa tana fadin "Barta inna Zulai! ki kyaleta ai anan zata kwana ko?da k'warank'watsa tunda har ta zageki yau bara tayi bacci lafiya ba……" Gantsarewa tayi jin an kamar an soka mata allura a baya takai hannu ta sosa ,tana gama sosawa taji wani gurin ya dauki k'aik'ayi sosawa ta kuma yi tare da daukar tabaryarta zata wuce !Cak ta tsaya tare da cire rigarta tana fadin "Laminde taimakan dan sosan bayana kinga ya karad'e da k'aik'ayi ……"

  Tabe baki Laminde tayi tana fad'in "Ke ni bana iya tab'a wannan hegen bayan naki da kike wata baki sa mashi ruwa ba ……"

  Ta bude baki zatayi bala'i taji kamar ana kara mata azaba a bayanta ……jikin bango ta matsa ta ci gaba da goga bayanta da karfi amma kamar ana karasa !Abu kamar wasa sae ga Jummai na birgima tsakar gida tana ihun k'aik'ai ……Ganin da gaske take yasa matan gidan fara taimaka mata ana sosa mata da cokulla tare da yan jik'e jik'e da aka yi ta d'ura mata ……Kusan awa biyu sannan azabar ta fara ragewa suka kamata suka shigar da ita daki ……

  Umma kam tana di'bar icce bata san wainar da ake toyawa ba sae da ta dawo sannan ta iske K'arama ta haye ruwan cikin wani yaro dan gidan Fulani tana jibga tare da ihu kamar ita yake duka ……Yara kuwa sun zagayesu sae dariya suke !Da kyar ta samu ta janye K'aramar daga jikinshi tana ihu ta shigar da ita cikin Bukkar su sannan ta ce "Me ya had'a ki dashi K'arama ?

  Dago kai tayi tana kallon Umman da rinannun idanunta tace "Ce man yayi Shegiya, meye Shegiya Umma?

  Shiru ta mata tana kallon idanunta sannan ta mike a sanyaye ta janyo wata kwaryar fura ta bude ta fara bata ……Bata damu ba ta fara sha tana lashe baki kafin ta bude baki tace "Ummana wa ya baki kanya da kika fita?

  Da sauri ta kalleta tana fadin "Ba wanda ya bani kanya K'arama"

  Tabe baki tayi tana kallon cikinta sannan tace "Kuma na ganta a cikinki yanzu ……?

  Da sauri ta buge mata baki tare da sakin kuka a hankali tana fadin "Ban hanaki Fadar haka ba K'arama? so kike mutane su tsane mu bayan azabar da muke ciki yanzu?Na shiga uku ni Hafsatu wace irin d'iyace haka Allah ya bani ?Ya Allah na roke ka bayyana *ABUNDA KE B'OYE* a tare da wannan d'iyar ko ma huta da azabar rayuwa……"

  Dafe Bak'inta tayi tana hararanta kasa kasa tare da fad'in "Ni kika daka Umma?

 Bata kalleta ba ta cigaba da kukanta a hankali tare da daga hannunta sama tana addu'a sannan ta juyo tana kallon K'arama da har lokacin ita take kallo ……

  Tsaki K'aramar ta saki a hankali tana hararan Uwar tata sannan tace "Dallah ni Bari kallona!Ina Ruwana dake ni ……"Ta karashe maganar tana watsa mata harara tare da jujjuya baki……

  Wani Sabon kuka ya k'wacewa Hafsuwalle najin abunda K'aramar take fada ta saka hannu tare da kifa mata mari tana fad'in "Ni kikewa Tsawa K'arama?

  Fashewa tayi da kuka ta mik'e tana tana kallon Umman tata lokaci guda ta saka hannu tare da duma mata K'ulli ta bar bukkar da gudun tsiya tana fad'in "Ai dai na rama "

  "Innalillahi wa'inna ilaihir raju'un "Hafsuwalle ke fada tare da dafe inda K'aramar ta daketa tana fitar da kuka gwanin ban tausayi ……


【】

 *M*a'aruf ko da ya koma gida ya fadawa Madre abunda ya faru " Wae wata aljanar yarinya ta mashi fitsari a jiki har yanzu gurin bai bar wari ba ji yake dama ana cire k'afa da yau yaje an cire tashi……"

 Dariya ta fara mashi don sam bata ji Haushin Yarinyar ba !Tana sane da yarda Ma'aruf ko daukar yara bayayi don kar su mashi fitsari……

  Kallonta yake kamar ya fasa mata kuka sannan ya kalli sumayya da ta shigo daga ita sae Three quater da blouse tana tambayar Madre abunda take wa dariya ……

  Aiko Madre din na fada mata ta hau dariya tare da rashewa saman rug din tana nunashi ……

   Kallon Madre yayi sannan ya kalli Sumayyar yana fadin "Bansan yaushe raini ya shiga tsakaninmu ba Sumayya"

  Nunoshi tayi da hannu tana kokarin danne dariyarta tare da fadin "Yaya Ma'aruf ana plastic surgery fa!

  Cikin tsawa yace "Wallahi ko ki bar nan gurin ko na maki shegen duka "

 Sanin zaya iya ne ya sata mikewa tana fadin "Allah ya baka hakuri" ta koma daki da gudu tana dariyarta ……

 Kallon Madre yayi yana fadin "Kin gani ko Madre wallahi sae na duki waccan yarinyar yau "

  Gintsewa tayi tana fadin "Allah ya baka hakuri Auta nima na daina"
 
  Shiru yayi ba tare da yace komae ba !Itama Madre din shiru tayi tana kallon Autan nata ganin ya lumshe idanu sannan ta shafo kanshi tana fadin "Sorry kaji ko Autana kaine da abun dariya wae aljana ta maka fitsari a jiki ……"

  Shiru ya mata tare da kwantar da kanshi saman kafadarta ya lumshe ido ……

  Sallamar yayarshi Maryam da yaranta biyu Afra da Ihsan ya sashi bude ido tare da sakin karamin tsaki ya na shirin mikewa ……

  Ihsan ta kwace hannunta daga na mamanta rugu ta hayeshi tana fadin "Oyoyo Uncle "

  Bata fuska yayi yana kallonta yace "Headache" a takaice

  Maryam kam gurin Madre ta nufa ta zauna yayin da Afrah ta rabe jikin kujera tare da sakin kuka da karfi ……

  Su duka suka kalleta kafin Madre tace "Zonan Afrah ya akai?

 Ma'aruf ta kalla sannan tace "Ba Uncle ke harara ta ba tunda muka shigo……"

  Hararan ya sake mata yana fadin "Zan bata maki rai Afrah yaushe na harareki……"

  Da gudu ta karasa jikinshi tana fadin "Uncle Baka Sona kullun nazo gidan nan sae ka harare ni dan Allah ka daina ina sonka kaji Uncle ……"

  Jikinshi yayi sanyi don ya tabbata da ya harareta !janyo ta jikinshi yayi yana fadin "Is okey kinji ko Afrah ……Ihsan ya dai?

  Madre kam dariya tayi tana kallon Maryam da ke ta faman korafin wae Auta ya bar Madre da Kumba a jiki ……




*HAJJA CE👈*
 *&*
*FEEDOHM💞*
[5:03PM, 12/1/2017] 💧💧 Feedohm💞: 𹰽𹰠*ABUNDA KE BOY'E……*
        《Almost True Life Story》

                   🍁🍁
                      💧

© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


        *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*
   *&*
*_K.A.S Precious HAJJA CE👈_*

*SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《Ummana》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
 *Da dukkan masu suna HAFSAT dake duniyarmu*


     Page *31-32*





     *F*uska a daure ya kalleta yana fad'in "Tunda gaki sae ki yanke mata……"
  Harara ta sakar mashi tana fad'in "Ni kake fad'awa magana Auta?Yaushe na fara wasa da kai ban sani ba……"

  Murmushi yayi mai sauti sannan yace " Allah ya baki hakuri Sister ……"
  Itama murmushin tayi tace "Madre yaushe mara kunyar Autanki ya sauka……?
  Shiru Madre din tayi tana kallonsu cike da kauna sannan tace " Bai je gidanki ba ranar friday?

  Da Sauri ya kalli Maryam din yana lagwabe kai tare da kanne mata ido daya ,Yar dariya ta saki ta juyar da kai tana kallon Madre sannan tace "Ihsan Uncle yazo ranar Friday……?

  Waro Ido yarinyar tayi tana girgiza kai alamu aa tare da bude baki ……
  "Ma'aruf……"Madre ta fada tana mashi kallon tuhuma

  "Madre ba na fada maki motar ne ya samu matsala kafin na karasa gidanta……"ya fada yana kokarin guduwa daga falon ……

 Jefa mashi pillow tayi tana girgiza kai cike da takaicin halinshi sannan ta juyo tana fadin "Sae da nace yaje gidanki ranar Friday ashe baije ba "

  "Bansan wane iri hali Gareshi ba Madre!Ina Sumayya take ne……"

   "Tana ciki yanzu Ma'aruf ya koreta……" Madre ta fada tana kallon dakin Sumayya……

  Dariya Maryam ta saki tana fadin "Madre anya ba yar gida za'ayi ba?don d'iyarki na son Autanki"

  Dariya Madre din tayi don ita kanta ta lura da take taken Sumayyar sannan suka shiga ba da firansu har Abbansu ya dawo suka gaisa……su Afrah da Ihsan kam kamar suna jira suka bishi part dinshi suka cika shi da shegen surutu don ma yana da son yara sossae……

  《》《》《》

  Har Dare ya take Hafsuwalle bata ga K'arama ta dawo ba sossae hankalinta ya tashi ta mike ta nufi inda take zama amma ko alamunta bata ji ba……
  Bayan gida ta leka amma wayam babu K'arama babu dalilinta a sanyaye ta dawo tana tunanin ko tana d'akin Lauratu ne !Ta dad'e tsaye tsakar gida tana sauraren ko zata ji motsinta amma shiru, Zulai ta fito rike da buta a hannu ta kalleta a wulakance ta watsar tana fad'in "Wane munafunci ake shiryawa anan kuma Hafsuwalle?ko jarabar ce ta tashi ake neman namiji!

  Shiru Hafsuwalle tayi sannan ta rab'e ta koma cikin Bukkarsu yayin da hankalinta ya k'ark'ata K'arama na dak'in Lauratu acan zata k'wana !Gabanta ya fad'i da ta tuna indae Mutanen gidan suka tabbatar da K'arama ta k'wana d'akin Lauratu to zasu sha wulakanci !Tunda a k'a'idar garin Amarya bata fitowa sae tayi sati d'aya haka babu wanda ke shigar mata dak'i har sae ta fara harkokin tsakar gida……

  Kwanciya tayi tana addu'ar Allah yasa K'aramar ta fito ba tare da ta k'wana ba !A haka bacci b'arawo ya kwasheta ……

  *K'*arama kuwa tunda ta ma Ummanta k'ulli a baya ta fice daga gidan !K'auyensu Malan Lado ta nufa da yake yanzu ta san hanya sarai bata buk'atar rakiyar wani ……
Ita Kad'ae ta yanki daji har ta isa garin sannan ta zagaye ta bayan gida ta shiga Bukkar Baffanta ……

  Kamar Kullum a kwance ta iskeshi idonshi na kallon sama d'akin sai doyi yake !Bata damu da warin d'akin ba tunda ba sani tayi ba ta rab'a ta tsallakeshi ta bude furar da Maitafasa ta kawo mashi ta fara sha !Tsaf ta shanyeta saboda yunwar da ta k'waso sannan ta kalli Lado tana fadin "Bara na karo wata sae na baka ko Baffa……?

 Ta mike da sauri ta bar d'akin !Lumshe ido yayi a ranshi yana fad'in " Karki Fita kin ji d'iyata!bana son wani abu ya sameki saboda ke kad'ae nake gani na samu sauki a rayuwata"Hawaye suka gangaro mashi ganin babu mai jin maganarshi ga K'aramar ta fice da gudu kuma yana jiyo Maganar Maitafasa da Kundum……

  Tana Fita ta iske Kundum na ma Maitafasa kitson Zanen Hannu Mai tafasar ta zage sae bala'i take wae Kundum ta matse ta a cinya ta sakar mata tusa ……
 Bahaggon salatin da Kundum ta saki shi yasa Maitafasa zabura ta mike tana fad'in " Amma Kundum anyi lalatarta!ina Macijin da kikewa wannan salatin na rafke shege tunda ke mata kika rako duniya"

 Juyawar da zatayi suka hada ido da K'arama dake tsaye tana dage gira tare da miko kwaryar fura……
  "Allah ka yafe man na kashe shegiyar nan kowa ya huta"Ta yayi tabaryar dake kusa da ita ta nufi K'arama zata doke……

  Ji kake Tim Maitafasa cikin makeken ruwan k'watar dake baje tsakar gidansu……
  Wata Dariya K'arama ta saki tare da tab'a hannu har da tsalle tana nuna Maitafasar dake kokarin tashi……
  "Amma wanga diya anyi hegeyi yanzu Maitafasar kikewa dariya don ta fad'a kwata?cewar Kundum tana kokarin gimtse tata dariyar muguntar

  "To bakar munafuka bud'e baki kiyi taki dariyar mana !Da kwarankwatsa na dade da sanin ke kundum algunguma ce……"Maitafasa ta fada tana kokarin mikewa amma kamar wasa taji cinyarta ta rike yayin da azaba ta fara mamaye cinyar……

  Jehowa K'aramar Tabarya tayi tana fad'in "Wallahi kika bari na tashi yau sae anyi sallar gawarki a garin nan……Sae na maki karyawar rashin mutunci "

  Dariya Kundum ta saki tana watsa hannu baya tace "A hayye su Maitafasa a cikin fitsarin shanu ……Yo ba k'ara inyi dariyata ba tunda abun naki ba mutunci "

  Ihu Maitafasa ta saki tare da rike cinyarta tana fad'in "Kundum taimaka kamar cinyar zata cire nake ji……"
   "Yo ta cire mana !Mai ya shafi Kundum bakar Munafuka……!Cewar kundum tare da tsallake Maitafasa ta shige makewayi babu ko buta……

  K'arama kuwa d'akin Maitafasa ta fad'a tana tsalle harda tab'a hannu ta dauko katuwar kwaryar da ta gani cike da fura ta koma d'akin da Lado yake ta fara bashi ……
Shi kanshi Ladon Yana mamakin yarinyar yarda take iya mashi komae ba tare da ta tambaya ba wani sa'in har tsoro take bashi saboda ko kad'an babu wanda zaice K'arama na iya bawa wani ko da abinci bare yarda take janye shinfidarshi ta canza mashi wata ta kuma gangaroshi sannan ta wurga kayan da ya bata tsakar gida ……Sae dae Maitafasa ta dauka ta wanke tana bala'in duk lokacin da ta kama mai canza mashi shinfida birni za'a rabasu……

  Wasa wasa maitafasa ta kasa tashi har Sae da Kundum ta tausaya mata ta kira makwabta aka kamata aka kaita d'akinta sannan ta lek'a ta kira mata wata tsohuwa dake d'auri tazo ta murji kafar ba tare da tasan menene ciwon ba ta tafi ……Ana gama murzar kafar wahalallan bacci ya kwasheta……

  K'arama kam batayi tunanin komawa k'auyensu ba ta rab'a gefenshi ta kwanta itama anan bacci ya d'auketa yayin da Malan Lado ya kura mata ido yana jin soyayyarta tare da tausayinta na ratsashi ji yake ina ma zaya iya daya fadawa duniya su bar sheganta mashi diya domin halalinshi ce……

【】

Ma'aruf kam Kafin Ya koma Madre tawa Abbanshi maganar tana son a hadashi Aure da Sumayya !Da fatan alkhairi Abban ya bisu don ya tabbata barata tab'a zab'awa Autansu mace ta banza ba !kuma yana da yak'inin Sumayya ta samo tarbiyya mai kyau tunda Hannunsu ta tashi ……

  Shi da kanshi yawa Ma'aruf din maganar ya bashi Sumayya !Wata irin faduwar gaba ya samu a ranar don ko kad'an bai tab'a tunanin zai auri Sumayyar ba beside ma bata cikin matan da yake tunanin aure !Sai dae ko kad'an baya iya gardama da iyayenshi ……Don haka kai tsaye ya amsa a baki sae dae a zuciyarshi kamar ta kone yake ji !Bai nuna ma kowa bai ji dad'in zab'in da iyayen nashi suka mashi ba sae dae ya barwa kanshi!
  Ko kwana biyu bai karayi ba ya tattara kayanshi ya koma india tun da lokacin saura 3 month ya dawo baki d'aya……kuma a yarda iyayen nashi suka fada da ya dawo za'ayi bikin nasu ……!



*HAJJA CE👈*
  *&*
*FEEDOHM💞*
[5:06PM, 12/1/2017] 💧💧 Feedohm💞: 💧💧 *ABUNDA KE BOY'E……*
        《Almost True Life Story》

                   🍁🍁
                      💧

© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


        *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*
   *&*
*_K.A.S Precious HAJJA CE👈_*

*SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《Ummana》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
 *Da dukkan masu suna HAFSAT dake duniyarmu*


    Page *33-34*



Sumayya kam Sai da ya tafi da kwana biyu sannan Madre ta fad'a mata !kamar zata mata sujjada dan murna babu kunya ta dinga wangale baki harda su rawa ta zama Mrs Ma'aruf……Madre kam da kallon mamaki ta bita tana jinjina rashin kunya irin na sumayya !!

  Ranar ta fadawa duk wasu friends nata har wad'and'a ta manta cewa ta zama Mrs Ma'aruf yayin da ta canza suna a dukka account dinta na social media zuwa Mrs Ma'aruf……

  Saboda bala'in zakewa ranar tama wata friend dinta Beeba waya wai ta kawo mata mai magungunan mata zata saya ta fara amfani dasu tun yanzu ……

    "Ikon Allah tun yanzu Sumayya?abunda Beeba ta fad'a kenan tana rike baki kamar tana gabanta

  "Kinga laifina ma kenan Beeba?Kawae ki samo man masu kyau ki kawo man yanzu, bana son nakai gobe ban fara amfani dasu ba……"

  "Allah ya kyauta "Abunda Beeba ta fad'a kenan ta yanke wayarta……

  Tsaki Sumayya ta saki ta matsa gaban madubi ta fesa turare sannan ta dauki wayar ta kira Ma'aruf, amma har ta kare ringing bai d'auka ba!ba kuma don bai ga kiran nata ba a'a hasalima wayar na bisa kirjinshi yayin da yake kwance rigingine yana kallon sama ……

  Kusan sau uku tana kiranshi bai d'auka ba sannan ta zauna ta rubuta gutun message ta tura mashi "  Please pick my call i wanna hear you rancid voice despite the fact you're the light that brighter my heart……It's Mrs Ma'aruf"

  Yana jin shigowar text din amma bai duba ba har sae da ta sake kiranshi sau biyu sannan ya d'auka ba tare da yayi magana ba ……

  Cikin Zumudi tace "Hello……"
      "Yaya Ma'aruf……"
      "Kana jina……?

 "Sumayya" ya fada a takaice……
  Cikin shagwaba tace "Shine kuma kayi shiru ka kyale ni……"

  "Bana son surutu me kike son fada……?ya fada a hankali idonshi a rufe

  "Allah ya baka hakuri Yaya Ma'aruf dama ina so ne na tambayeka zan dan fita idan beeba tazo na rakata inda take aje motarta tunda naga yanzu na zama matarka komae kai ya kamata nemi izini gurinka……"

  Dariya da takaicinta suka dirar mashi lokaci guda har bai san lokacin da yace "Uban wa yace kin zama matata ki kirani ki tambayeni idan zaki fita Sumayya?ya karashe cikin sanyin muryarshi amma a nashi tunanin fad'a yake ……

  "Madre tace an baka ni……kuma laifine don na tambayi mijina zan fita?ta fad'a a shagwabe……

  Yanke wayar yayi tare da bin ta da harara !Shi kam an hadashi da bala'i wallahi !abunda ya fad'a kenan a fili tare da jan karamin tsaki……
  Ita kam Sumayya bata ji komae ba illa tsallen da tayi ta fad'a saman gado tana juyi ita kadae……

 【】

  "Uban wa na kama yanzu ……"Cewar Matar Fulani tare da cakumo wuyan K'arama da ke zaune gurin kuka tayi bud'u bud'u da ita kamar ba gobe……

  Ido ta k'walalo mata tana kokarin aje k'aton dutsen dake goye a bayanta tana fadin "Ni kika kama!
  Duka ta sakar mata akai tana fad'in "Uban me ya hadaki da Jabiru……?

  Turo baki tayi tana dafe inda ta bugeta tace "Ba shi bane ya ce man shegiya……"

  Kara dukanta tayi tana fadin "Karya ya maki dan ubanki ba shegiyar bace !uban waye bai san amanar Malan lado aka ci ba aka haifeki" ta karashe maganar tare da hankad'ata ta fad'a ta zauna kasa tana harba kafafuwa ……

  Juyawa Matar Fulani tayi tana zage zagenta !K'arama kam dutsen dake bayanta ta dauka yayin da ta saita duwawun Matar fulani ta jefa mata ta watsa da gudunta ta bar gurin……

  Dafe gurin tayi ta juyo amma babu K'arama babu dalilinta wani uban zafi ta ji ya soketa kamar lokacin aka jefa mata shi ,ta d'aga kai ta kalli kukar da ke kusa da ita tana luliya gurin ……
  Mace ta hango sama tana washe mata baki hakora a waje kamar na shanu……
  Kwaryar nononta ta saki tare da dafe kai ta baza da gudu ta koma gida tana dafe da inda K'arama ta jefeta……

  Ranar da Lauratu ta fara fitowa ranar matan gidan a waje suka shinfida buhu suka zauna duk da azabar ranar da ake ……Jira kawae suke Lauratun ta nufi Bukkar da Hafsuwalle take su fadawa Ard'o ya mata rashin mutunci Tunda yanzu ta zama karkashin Garka ta fita daga hannun Hafsuwallen……

  Tana lura dasu don haka ko bukkar bata kalla ba har Sae da K'arama tazo ta raba kusa da ita ta zauna tana washe mata tace "Yaya Laulatu har an gama dafa ki a d'akin?

  Kallon mutanen gidan tayi taga kowa ya zuba ido yaji ko zata mata magana !hawaye suka taru a idonta ita dai bata jin zata iya k'yale K'arama ko da za'a fidda mata rai ne ……
  Goge hawayen tayi ba tare da tace komae ba ta janyo K'arama jikinta ta rungumi ita kanta ta san tayi rashin kanwarta……

  "Shikenan Lauratu yanzu Ard'o bai isa ya saka doka ki bita ba?cewar matan gidan kamar hadin baki ……

  Kuka ya kwace mata tace "Wallahi bazan iya rayuwa babu K'arama ba a kusa dani dan Allah ku barni da ita"

  "Idan Ard'on yazo sae ki fada mashi haka……"Cewar Laminde tare da nade buhunta don dama abunda take jira kenan……

  Hafsuwalle ta leko tare da kiran K'arama don duk abunda suke tana saurarensu ……Cikin Sa'a K'arama taje ta sakata Bukka da wayau da dubara ta zaunar da ita tana mata tatsuniya ……

  Inno kam girgiza kai tayi a hankali don har ga Allah abunda akewa su Hafsuwalle ya fara isarta kawae tana daurewa ne don babu uwar da zata ce bata son d'iyarta a duniyar nan ……Ko da Ard'o ya dawo suka fada mashi banza ya masu saboda yana jin Kunyar Lauratun yanzu tuda ta rigaya ta zama surukarshi !

  Tun daga lokacin Hafsuwalle ta daina barin K'arama na yawan shishshigewa Lauratun saboda matsalar cikin gidan ……Tun tana mata kuka idan ta sakata bukka har ta daina saboda ko'ina Umman zataje sae ta ja hannunta su tafi ……

  K'arama kam ganin Umman tata na lallabata yasa ta itama take jin maganarta sossae amma hakan baya hana idan ta daketa ta mike ta rama ta gudu ga rashi kunya duk lokacin da abun ya kad'o mata ……
  Mutanen gidan ma bata ragawa duk wanda ya daketa sae ta rama idan kuma bata samu ramawa ba to kai kuma ranar baka bacci ……zaka kwana kana ihu ana baka tsoro! hakan bai saka sun daina takura masu ba don basuyi tunanin saboda ita ake basu tsoro ba ……

  Maganar Idan kaci abu ka fito ta kalli cikinka tace ga abunda kaci har lokacin bata daina ba sae dae ta kanci dan banzan duka gurin tsofaffin garin wata rana……

   *Two month later……*

  Tana bayan umman ta sun debo ruwa sae uban surutu take kamar an bude fanfo ……Aje tulun tayi ta juya baya da gudu tare da leka Zauren wani gida da aka saki buhun kofar Sannan ta matso kusa da Ummanta tana tab'a hannu had'i da tab'e baki ……
  "Umma jiya Habi Surukar Fulani tace man wae yar iska……"ta a fad'a idonta na kan zauren

  A Sanyaye Umman ta kalleta tana girgiza kai saboda ta san wani abun take shirin aikatawa……
   Hade hannu tayi sannan ta dauki tulun ruwanta tayi gaba abunta tana murmushi……Tana ajewa kafin Umma ta shiga d'aki ta aje Zanin lullubinta ta fito ta shige kewaye ta dire ta katanga ta bar gidan……

  Gidan Fulani ta isa ta tarad da Habi da Matar Fulani suna sussukar masara ……
  Da yar ficiciyar muryata tayi sallama ta mak'ale zauren gidan ba tare da ta shiga ba ……

  "Wacece nan ta labe…?cewar Habi
 "K'arama yar iska ce ……"ta fada tare da yin tsalle daya ta fado cikin gidan ……

  A Harzuke matar fulani ta matso tana fadin "Ke ce dama ?Uban me ya kawoki gidannan ?Wae Habi bance kar wannan shegiyar yarinyar ta kuma shigowa gidan nan ba?

  Kyafta idanu ta farayi tana fadin "Babban d'an iska na gani a zauren malan bashe shine nazo na fad'awa matar d'an iska da surukar d'an iska……"ta karashe maganar tare da rike kugu tana girgiza kamar wata budurwa……

  Kamar ta saka masu gas haka suka hayyako mata ta kwasa da gudu ta bar lungun……




*HAJJA CE👈*
*&*
*FEEDOHM💞*
[7:51PM, 12/2/2017] 💧💧 Feedohm💞: 💧💧 *ABUNDA KE BOY'E……*
        《Almost True Life Story》

                   🍁🍁
                      💧

© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


        *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*
   *&*
*_K.A.S Precious HAJJA CE👈_*

*SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《Ummana》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
 *Da dukkan masu suna HAFSAT dake duniyarmu*


     Page *37-38*


     *S*ai da ya kammala komai sannan focal person d'in shi ya kai shi can airport ya hau jirgin zuwa kano, tun a hanya yayi waya aka turo mai da drive. Suna dira ya hango parado d'in shi da ya siya a ita aka zo d'aukar shi ya k'arasa yashiga driver yaja, har suka je gida amsa wayoyi yake yi direct ya wuce side d'in Madre kai da ka ganshi kasan a gajiye yake ya zauna kan sofa tare da killar da phone d'in shi a gefe ya rintsa ido.

"Ma'aruf ka dawo ke nan?" Madre ta fad'a tana k'okarin fitowa daga kitchen. Amsawa yayi a wahale har ta k'araso kusa dashi tana kallon shi cike da tausa yawa dan ta hango gajiya sosai a fuskar shi.

"Toh kaje kayi wanka sai na turo Sumayya ta kawo ma abinci, da kaci sai ka kwanta ka huta..." Da sauri ya hau gir-giza kai alamar a'a cikin turo baki tamkar karamin yaro yace, "no Madre please karki turo min ita wallahi ciwon kai zata samin, ko ta tambaye ki na dawo kice mata a'ah kawai."

Yana kaiwa nan ya mike yayi hanyar fita, yana jiyo Madre na cewa, "a'ah yaro ni kam ban iya karar  ku ba, idan ta tambaye ni Zan gaya mata gaskiya."

Yana shiga ya fad'a kan rog yana sauke numfashi, gaba d'aya abinda ya faru da lado ne yake mai yawo yana mamaki ace wai kishiyar uwar ka ita ce zata illataka sabida wani sakar ci, sai yanzu yake jin haushi da be tsaya yasa an hukunta Hansai ba amma ya bar shi har zuwa lokacin da zai koma garin.

Mtww... *!* yaja tsaki tare dayin juyi bayan ya tuno cewar kwanakin bikin shi sun kusa zuwa shi bama wanda ya sanarwa, mtww... *!* ya kuma jan wani tsakin tare da mik'ewa tsaye ya shiga bathroom bayan ya rage kayan jikin shi.

Daga shi sai small towel a kugunshi ya fito, tunda ya bud'e bathroom d'in ko'ina na cikin d'akin ya fara fitar da wani daddad'an kamshi me azabtar da zuciya, dressing mirrow ya k'arasa ya d'auki wani k'aramin towel d'in wanda yafi na jikin shi kan-kanta ya fara goge jikin shi dashi, yana gamawa ya fara shafa mayuka masu  tsada da kamshi sannan ya wuce dressing room ya fito da sweetshit green color da jeans white color ya sanya yasa takalmi trainer's kalar green ya feshesu da kala-kalan turaruka masu masifar kamshi ya sanya ear muffs a kunnan shi yana jin suratul tauba a haka ya shiga side d'in Madre.

Zaune ya same ta tana danna laptop gefenta duk takadda ya k'arasa ya zauna a 2seater tare da kallon ta yana turo baki like small boy. "Kaje dining kaci abinci." Kurum Madre ta ce mai ba tare da tad'ago ta kalle shi ba dan tasan idan ta d'ago me zata gani.

K'in tashi yayi sabida beji abinda take cewa ba sakamakwan ear muffs d'in dake kunnan shi, a hankali ta kalleshi tayi mai alamar ya cire da hannu sannan yayi yadda tace d'in but still bakin shi a zumbure ta ta6e baki tare da cewa,

"Kaje kaci abinci nace ka dawo daga tafiya kak'i bawa ciki hakk'in shi, ko a koshe kake?" Ta tambaye shi tana ture laptop d'in gabanta, Ma'aruf ya gir-giza kai tare da cewa.

"Please Madre muje ki bani..." Kallon shi tayi da mamaki sannan ta mik'e tayi hanyar dining d'in tana cewa, "ni gara ma kayi auran Ma'aruf na ga alamar yanzu tabarar taka neman yin yawa take yi...."

A baya ya bita yaja kujera ya zauna, sakwara da miya ta zuba mai wadda taji nama da stock fish ga uban ogu leave sai kamshi ke faman tashi ta zuba mai lemon kwakwa da ya sha peak milk ya wanke hannu a cikin boul d'in dake gurin ya fara ci kenan sai ga Sumayya ta dawo.

"Oyo-yo Yaya Ma'aruf dama yau zaka dawo?" Cewar Sumayya tana k'arasowa wajan shi da sauri cikin farin ciki da murnar ganin shi da tayi... Banza da ita yayi yana ci gaba da cin abincin shi tamkar be jita ba har ta k'arasa kusa dashi taja kujera a kusa dashi ta zauna.

"Welcome Yaya Ma'aruf..." Ta sake fad'a ya sa 'yar k'aramar sakwarar da ya gutsuro a cikin bakin shi kafin ya tauna ya had'iye yace "thanks..." Cikin ranta tace "thanks kuma kai da zaka ce min OK ko yauwa sai kace wani thanks sai kace nayi ma kiss..." A fili kuma tayi murmushi tare da kura mai ido, ba k'aramin kyau yayi mata ba, ji take inama zai tsaya da ta rungume shi taji shi a jikinta wannan pink red d'in lips d'in nashi ba abunda zai hanata d'ora nata akai ta lumshe idanu ta bud'e su tar akan nashi....

"Yaya Ma'aruf ina ta maka zancen different event d'in da za'ayi kayi shiru baka ce min komai ba, dan Allah yau karka tashi bamu gama magana ba." Duk abinda suke yi Madre na jinsu, har mamakin Sumayya take yi irin yadda taji tana zuba surutu kuma duk akan yadda bikin su zai kasan ce ne, shi kuwa gogwan yayi shiru sai faman cin sakwarar shi yake tamkar jariri ake bamawa. Da yaji surutun nata yayi yawa ne yasa shi kallonta da manyan sexy eye d'in shi yace.

"Sumy... *!*, wai ba kya gajiya da surutu ne...? And ina cin abinci kike son muyi magana da yake haka aka yi teaching d'inki...? Bana son hayaniya kije ku shirya kome zaku yi I don't have a time to talk akan wannan abun abi..?"

Bata wani ji haushi ba ta d'aga mai kai tare da m'ik'ewa tabar gurin hannunta rik'e da wata leda mai d'auke da magungunan mata da taje Beeba ta rakata suka siyo gidan wata hajiya mai komai da ruwanki. Da kallo ya bita har ta shiga room d'inta ya gir-giza kai tare da wanke hannun shi dan appertained d'in shi nacin ya gishe.

Sumayya na shiga d'aki ta zube kayan akan gado sun fi kala ashirin ko wanne da amfanin shi ta d'auki wata katuwar jarka ta fara kwankwad'ar abunda ke ciki ko rashin dad'in ba taji ba har tasha rabi sannan ta d'auki wasu ta fara cusawa a ppt d'inta da Cotton wood.... Lol amarya.












*FEEDOHM*💞
&
*HAJJA CE*👈
[7:51PM, 12/2/2017] 💧💧 Feedohm💞: 💧💧 *ABUNDA KE BOY'E……*
        《Almost True Life Story》

                   🍁🍁
                      💧

© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


        *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*
   *&*
*_K.A.S Precious HAJJA CE👈_*

*SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《Ummana》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
 *Da dukkan masu suna HAFSAT dake duniyarmu*


     Page *39-40*


*FEW MONTH LITTER*

    *G*idan cike yake da 'yan uwa da abokan arziki na both amarya da ango, Madre bak'i yaki rufuwa ana aurar da auta duk inda ka ganta bakin ta da murmushi ta k'awayanta na gurin aikin su sai zolayarta suke sai dai tayi dariya kawai ta wuce dan murnar da take ciki tafi komai yawa a zuciyar ta.

Tana fitowa compound ta hango Ma'aruf yaji uwar kwalliya kai da ka ganshi kasan cewar shine ango, abokan shi guda uku suna biye dashi suma duk sunsha ado Madre ta sakar mai murmushi tare da komawa cikin d'aki dan kar mutane suga zak'ewarta a tafi ana yi da ita abaki. Waje suka fita inda maza suke manyan mutane da kananun ma'aikata kai da gaka tarun kasan ba k'aramin people ya tara ba, Ma'aruf yayi mamaki dan shi yasan ba wani invitation card ya raba ba amma kakaf abokanshi na k'asashen waje dana gida Nigeria d'ai-d'ai kune babu "Toh waya sanar musu..? Ya tambayi zuciyar shi amma ba amsa "ko Naseer ne yayi mai wannan aika-aikar...?" Ya juya yana kallon Naseer dake ta faman gaisawa da mutane "amma kuwa idan shine sai ya yi mai rashin M." Ya fad'a a cikin zuciyar shi sannan ya fara smiling yana gaisawa da mutane.

Kunnuwan shine suka jiyo mishi ana cewa an d'aura auran Muhammadu Ma'aruf da Sumayya akan sadaki dubu d'ari biyu da mukullin mota.... Daram-Dam... *!* k'irjin shi ya buga cikin ranshi yace "Dubu d'ari biyu sadaki...? Waye yace musu zai bada har wannan kud'in shi da yake son albarka aure, uwa uba harda car key shi da beyi niyar siyawa Sumayya mota yanzu ba sai yaga irin takunta.."

Saleem ne ya ta6o kafad'ar shi ganin tamkar be san an shafa fatiha ba yayi figigit yana kallon shi kafin shima yakai tafin hannunshi masu tsananin taushi ya shafa fuskar shi "kai Ma'aruf ka saki jiki mutane sai kallonka suke yi sai suyi tunanin baka son auran please dan Allah."

Fitar da komai yayi daga ranshi aka fara gudanar da taro cikin kwanciyar hankali, sai da abokan shi suka fara tafiya sannan ya samu damar shiga cikin side d'in shi su da su Naseer sai tsiya suke mai yak'i kula su. Yana zuwa ya cire babbar rigar dama duk ta isheshi jiyake tamkar an d'aura mai katon dotse yayi saurin shiga bathroom ya fad'a cikin jarcuxe yana sauke ajiyar zuciya "ikon Allah..." Ya furta cikin ranshi "wai yau shi ake d'aurawa aure..? Ikon Allah shi be ta6a kawowa zai yi aure kusa haka ba sai gashi lallai kar mutum yaja da ikon Allah, shine mai komai sannan mai yin komai. Ya dad'e a cikin ruwan kafin ya fito ya sanya bathrobe ya wuce dressing room, nan d'in ma sai da ya dad'e sannan ya fito cikin shirin shi. Shadda ce yasa ash color tazarce tayi mai bala'in kyau ya fita parlor su Yaseer, Naseer da Sameer sai tsiya suke mai yana musu murmushi. Yana zama su Hidaya suka shigo da warmers na abinci suka dire musu suna kallon su, "uncle Ma'ar gashi nan inji Madre tace za'a kawo sinasir yanzu..."

Wani mugun kallo ya bisu dashi jin sunan da suke kiranshi a gaban friends d'in shi "Tasleema bana ce kar wanda ya sake kirana da wannan stupid name d'in ba..?" Ya fad'a ranshi a had'a suka fara kalon juna Hidaya tace "sorry uncle Ma'ar... Sai tayi saurin rufe baki jin ta sake fad'a ya kallesu tare da nuna musu kofar da suka shigo yace "get out... *!* marasa kunya kawai." Fita suka yi suna dariya Inteesar tace "ah su uncle angon Yaya Sumy gaskiya sun yi perfect wallahi, matsalar d'aya da Yaya Sumy zata sha fama miskilanci..." Suka kuma sakin dariya sannan suka shiga cikin d'aki gurin amarya.

Zaune suka same ta ana mata makeup duk kawayan ta suma suna tayin nasu, kallonta suka yi inteesar tace "gaskiya Yaya Sumayya kin yi dace da miji, uncle Ma'aruf ya had'u ta ko ina kinga kyawun da yayi kuwa yanzu...? Hidaya ta kar6e zancen "wallahi uncle handsome guy ne ya had'a komai a rayuwa." Tasleema tace "kyau, ilimi, nasaba, kud'i, daraja, biyayya, tausayi, in fact shi have everything what I mean komai da komai..."

Wani kayataccen murmushi ta saki tare da sauke ajiyar zuciya lokacin an gama makeup ta mike tasa wata doguwar riga bridal tace "intee yana ina yanzun...?" Inteesar tace "yana side d'inshi tare da friends nasha.." Sumayya ta kalli Beeba "please Beeba d'akko min wannan turaran." Beeba ta kalleta da mamaki tace "kin san dai ba yanzu zaki amfani dashi ba sai an kaiki gidan miji uwar zumud'i kawai.."

Ganin Beeba ta hanata yasa tayi tsaki, ita yanzu so take kawai ta ganta a gurin shi sabida ta tsuma ga wanda Madre tayi mata ga wad'an da tasha a 6oye hakan yasa duk take jinta wani iri tana jin tamkar takai kanta sai dai yawan mutane yasa ta kasa zuwa. 8:00pm aka fara tafiya dinner wanda daga an gama an dawo za'akai amarya.

"Ma'aruf kaje ka shiga mota ana jiran ka kaji ko....?" Madre da ta shigo d'akin shi ta fad'a dan gaba d'aya event din da aka yi sai tazo ta sashi yake fita. Yanzu ma be so zuwa ba shi yasa tazo ta mai magana, yana jin haushi haka ya shirya cikin wani shegen yadi milk color da ratsin blue ajiki, hula yasa zanna blue da shoe cover yayi kyau sannan su Sameer suka kai shi motar da aka tanadar musu shi da anarya.

A ciki ya sameta gaba d'aya kamshin turare dana khumra sun turare motar, Ma'aruf kenan, yana matukar son kanshi hakan yasa yayi tasiri a zuciyar shi ya zauna kusa da ita tare da matsawa jikinta ya riko hannunta, jikin ta ya fara rawa nan da nan taso rud'ewa kamar ya gane ya janyo ta jikin shi yana kara shakar kamshinta a haka aka ja mota......













*FEEDOHM*💞
&
*HAJJA CE*👈
[9:25PM, 12/13/2017] 💧💧 Feedohm💞: 💧💧 *ABUNDA KE BOY'E……*
        《Almost True Life Story》

                   🍁🍁
                      💧

© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


        *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*
   *&*
*_K.A.S Precious HAJJA CE👈_*

*SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《Ummana》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
 *Da dukkan masu suna HAFSAT dake duniyarmu*



       Page *41-42*


        *D*inner akayi ta kece raini kowa ya ci ya sha daga abunda aka tanadar yayin da Madre tayi barin kudi kamar ita ke bugasu……Sae kusan 10 Na dare sannan aka tashi gidan Madre din aka koma kafin zuwa Safe ayi walima Ango ya tafi da amaryarshi don ba'a bukatar yan kai amarya ……

  Tunda Asuba aka fara shirya shiryen walimar AA Event & Design dake kabo crescent off Ahmadu bello way Garki 900242 Abuja ……Madre ta dauko sukayi decorating harabar gidan ……
     Sun kawata gurim sossae ta yarda ko makiyi bara ya kushe ba ……Karfe 4:10pm aka fito da Amarya Sumayya sanye da Arfo Lace white da ratsin Baki a jiki……tayi masifar kyau sai sheki take tana sargale da hannu Ma'aruf shima kanshi abun kallone Sae dae kallo daya zaka mashi ka tabbatar da murmushin Yaken dake kwance a saman kyakykyawar fuskarshi sab'anin Sumayya dake murmushin farinciki ……

  Sae da suka fara zuwa suka gayyar da dagin Abbah sannan suka koma ga dangin Madre suka saka masu albarka sannan suka koma inda aka tanadar masu kujerunsu suka zauna ……Yayin da sauti mai taushi ya karad'e gurin……

  Wajen magrib sannan jama'a suka fara watsewa yayin da Madre taki yarda tawa Ma'aruf nasiha ta koma part din Ma'aruf tayi kwanciyarta sae dae Abba da Maryam kadae suka masu Sannan suka ce ya dauki matarshi su tafi……

  Ko irin kukan da ake Sumayya bata yi illa murmushin da take tana yake hakora duk da irin sharrin da abokan wasa ke mata……Bangaren Ma'aruf kam yarda kasan shine Amaryar haka ya koma kallon mutanen gurin yake kamar ya fasa kuka yana neman Madre amma sam bai ganta ba !kasa hakura yayi ya kira Maryam ya tambayeta "Ina Madre?

  Ita Kanta tasan Madre boyewa tayi saboda son Autan nata sae dae ta kalleshi cikin kwarin guiwa tace "Auta Hidima tawa Madre yawa tana can gurin Family din su Abba suna kara gaisawa"
  Daga haka ta ja hannunshi k'annan Madre suka rufa masu baya har kusa da sabowar motarshi da Abbah ya bashi yau suka shiga suka tafi ……

  Haka suka isa gidanshi dake GRA wanda tun daga waje zaka gane tsaruwar da gidan yayi ……
  Baban falon gidan dake dauke da Royal chairs suka samu masauki yayin da ya zube saman three siter ya dafe kanshi dake masifar sara mashi ……Ita kam Sumayya tsaye tayi ta ware hannaye tana juyi a hankali tare da karewa falon kallo har tsawon minti goma sannan ta dawo ta zauna saman hannun kujeran tare da dafa bayanshi tayi kasa da kanta ta kira sunanshi ……
  Dagowa yayi ya kalleta sannan ya da kamo hannunta ya dawo da ita gefenshi ya zaunar da ita ya mayar da kanshi ya tallabe tare da lumshe ido ……

   " Yaya Ma'aruf yunwa fa nake ji ……"ta fada lokacin da ta kai hannunta ta shafa sajenshi ……

  Shiru ya mata ya sauko wayarshi ya typer message ya tura sannan ya kalleta yace "Ki jira ga Ahmed nan zuwa "

  Turo baki tayi tace "Aa ba sae ya zo ba gaskia na daina jin yunwar……!

  A Hankali ya kalleta yace "Why?

  Kai tsaye tace "Wannan lokacin bai kamata kowa ya shigo mana gida ba !

  Ya bude baki da niyar mata magana yaji karar doorbell ya mike ya nufi kofar ……Ahmed ya gani rike da leda ya mika mashi tare da mashi bankwana ya juya ……

  Ko da yazo gabanta ya aje ledar ya juya ya shige part din dake kallon tsakiyar falon abunshi ……

 ,Ita kam Sumayya gyara zama tayi ta fara cin naman kajin dake ciki sannan ta kwankwadi Fresh milk tare da lumshe ido sannan ta mike ta nufi handbag din ta ta fito da wani ruwan magani ta shanye tas ta aje robar ta kara janyo wani dunk'ulen bak'in abu kamar curin dawo ta fara ci tana yatsina fuska saboda masifar d'acin da abun ke da shi ……Wasa wasa sae da ta fiddo kalaluwar magani kusan Biyar ta cinye sannan ta mike tana mika ta tsallake ledar kajin ta nufi Part din ta taga Ma'aruf ya nufa ……

  Tsaye ta iskeshi gaban mirrow daure da towel yana combing din sumarshi !Ta cikin mirrow din ya hangota ya dauke kai kamar bai ganta ba ……

  Murmushi tayi sannan ta fada toilet rike da handbag dinta a hannu!shi kam tab'e baki yayi ya d'auko jallabiya fara k'al ya sanya tare da shinfida prayer mat ya kabbara sallah ……

  Koda Sumayya ta shiga toilet inserting magunguna ta fara yi kamar hauka sannan tayi wanka ta fito daure da towel a k'irji lokacin har ya sallame sallarshi har ya koma ya kwanta saman gado abunshi ……

  Daga bakin toilet din ta saki Towel dinta ta hawo gadon ta kwanta bayanshi saboda masifar feelings din da take ji saboda kayan matan da ta kwankwada ……
    Gabanshi yayi masifar faduwa take ya fara tunanin anya Sumayya bata bin maza kuwa?Wani bangaren na zuciyarshi ya bashi amsa da ina zata gansu bayan kullun Madre na tsare da ita a gida ……

  Kiran sunanshi da tayi ya katse mashi tunaninshi yayin da ta fara fad'in "Sorry Bana iya kwana da kaya a jikina bayana ke rashes"

  Gyada mata kai yayi ba tare da ya juyo ba !Ita kam hakan bai hanata yawo da hannunta saman kirjinshi ba tare da daura kanta a bisa wuyanshi ……

  Duk irin yarda yaso ya daure kasawa yayi dole ya juya ya fara mayar mata da martani yayin da ta fara fita hayyacinta tana kiran sunanshi cikin Zakuwa ……


  《》《》《》《》

  Hankalinta ta mayar Kan Sallau dake tambayar Lauratu ina zata je ……

  Cikin ladabi Lauratun tace "Zan je na duba Baffa ne da jiki "

  Daure fuska Sallau yayi yana kallon Fuskar Lauratu da tayi wa ado da kwalli tare da uban jan baki har saman goshi sannan ya kalli K'arama dake rike da hannun Lauratun tana lilo yace "Haba Lauratu Ahaka zaki fita mazan waje su kalle man ke fisabilillahi?

  Shiru Lauratun tayi tana kallon K'asa yayin da K'arama ta sheke da dariya tace "Amma ko an cuci maza !Yaya Lauratu me zasu kalla da fuskanki duk bak'in kwalli?ni dai mu tafi "

  Da yake ya san halin K'aramar bai ce mata komae ba ya kalli Lauratun cikin sanyin murya yace "Ki Taimakeni Lauratu karki fita da wannan kwalliyar ko wa ya kallah sannan dan girman Allahi ki saka katon Zani ki kulle duk jikinki ki zo muje na rakaku ku ganoshi mu dawo "

  Gyada kai Lauratun tayi sannan ta koma daki ta goge kwalliyarta tare da dauko katon Zani ta lulluba ta sake fitowa ta iskeshi shi kadae ……Cikin sanyin murya tace "K'arama fa?

  Kafin ya bata amsa suka hango K'arama ta fito daga dakin Zulai rike da katuwar kwarya ta nufi bukkarsu ta aje sannan ta ja ta tsaya bakin kofar gidan tare da juya masu baya ……

  Zulai kam fitowa tayi daka bandaki ko buta babu ta wurgawa K'aramar harara kamar wata kishiyarta sannan ta shige daki tana waka a hankali ……




  *HAJJA CE*👈
&
*FEEDOHM💞*
[5:54AM, 12/14/2017] 💧💧 Feedohm💞: 💧💧 *ABUNDA KE BOY'E……*
        《Almost True Life Story》

                   🍁🍁
                      💧

© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


        *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*
   *&*
*_K.A.S Precious HAJJA CE👈_*

*SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《Ummana》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
 *Da dukkan masu suna HAFSAT dake duniyarmu*



     Page *43-44*


Da Sauri Lauratu ta nufi gurin K'aramar taja hannunta suka fita yayin da sallau ya mara masu baya kamar wani mai gadinsu yanayi yana kare Lauratun gudun kar yan garin Su kalle mashi mata sannan duk wani motsinta saman idonshi takeyi !Ita kam hankalinta naga K'arama dake ta faman fitar da numfashi kamar namijin zaki……

  Suna shiga gidan suka iske gidan cike da jama'a an zagaye Lado dake kwance a tsakar gida yayin da maitafasa ke tsaye tana ta zuba ruwan tijara ita kadae ……
  Sallamarsu ce ta saka matan garin fad'in "Gasu nan ma Maitafasa"

  Ta watsa hannuwa baya ta nufosu ta cakumi wuyan K'aramar ta dire kusa da Malan Lado tana fadin "Kalli Fuskar wanga d'iya Lado ta gidan Ubanka tayi kama da zuri'armu da zaka fada man cewa d'iyarka ce "

  A Sanyaye yana Zubar da hawaye yace "Wallahi Inna wannan d'iyar jinina ce "

  "Lado banda mutunci fa !da kwarankwatsa ka k'ara maimaita wannan zancen sae na zabga maka mari a kumatunka duk da kake haka "ta karashe maganar tare da dungure mashi keya ……

  Tab'e Baki Kundum tayi tana fadin "Ba'a banza ba Lado ya amshi wannan d'iyar ba Maitafasa……"

  Juyowa tayi tana karkad'a yatsu tace " Fad'a man  a me ya amsheta algunguma? Yatsina hanci Kundum tayi ta juya k'eya ba tare da tace komae ba sae uban tsokin da ta ja……

  Wata mata dake tsaye cikin garke tace "Taya bara ya amsa ba bayan ita kanta yarinyar Mayya ce "

  Da Sauri Maitafasa ta saki wuyan K'arama tare da dafe kirji tana fadin "Raba ni da aikin mayu !Ke Lauratu "

  Daga kai Lauratun tayi ta kalleta sannan ta kalli K'arama dake ta raba ido tana kallon mutanen gurin !ta d'aga k'afa zata isa gurin Sallau ya kamo hannunta yace "Zan Dauki komae a duniyar nan amma banda cin zarafinki Lauratu "

  Kallonshi tayi da idanunta da suka ciko da kwallah ta gyad'a kai a hankali sannan ta zame hannunta daga rik'on da ya mata ta nufi inda su Maitafasar ke tsaye ta kama hannun K'arama ta rike ……

  Ihu Kundum ta saki tare da zubewa k'asa tana fadin "Dan Allah kiyi Hakuri karki cinyeni yar nan "

  Mutanen gidan suka dauki bahaggun salati mara karshe suna fadin "Shi kenan ta kama Kundum" yayin da suka yo kan K'aramar suka danketa kamar wata katuwar Mace suna fad'in "Wallahi Sae kin tsallaka ta munafukar yarinya daga zuwa zaki kama ta" wata ta kai mata rankwashi a tsakiyar kai ……

  Dafe gurin tayi tana turo baki tace "Wace?

  Uban rankwashi Maitafasa ta kuma kai mata tana fadin "Hafsuwalle ce dan ubanki "tare da watsa bak'in hannunta saman fuskarta sannan ta kashe ta da mari lokaci guda ta ta cakumi kwalar rigarta ta d'aga ta sama ta tsallake Kundum da ita sannan ta direta k'asa cikin mugunta da zulunci ……

  A Jiyar Zuciya Kundum ta saki ta mike zumbur ta nufi bukkarta tana d'angyasa kafa rike da kirjinta tana hucin wahala tare da zare idanu ……

  K'arama kam kuka ta saki da karfi saboda yarda Maitafasa ta direta k'asa har sai da dutsi ya fasa mata tafin kafarta !Yayin da Lauratu ta rungumeta da sauri tana kuka ta nufi Hanyar barin gidan da ita !amma mugayen matan dake zagaye da gidan suka fara dukansu suna fadin " munafuka……"

  Sallau dake tsaye bakin Zaure ya karaso cikin gidan ya zame masu kamar Mahaukaci ya kwaci Matarshi ya rungume suka bar kauyen yayin da ita kuma tana rungume da K'arama dake ta faman tsuka tana goge hawayenta!

  Kundum kuwa na shiga daki ta fara karkada jimammen kugunta tana gwatso tare da gwalo !Ji tayi kamar ana dukan fatar jima a kasa !bata damu ba ta janyo wani kodadden zani zata daura lokaci guda dakin ya kauraye da duhu yayin da ta gwalalo ido waje tana lalubar kofa amma ta rasa ta……

   Cikin dauriya ta fara karanto addu'ar su ta jahilai mutanen da "Yar kyalwa baiwaye dakin Kunduma tantar tantar yar kyalwa kunna hitila ……"

  K'arama ta gani duke gurin kafarta yayin da ta kama agararta ta ja cikin mugunta ……

  Cikin jin haushi Kundum tace "Awo kece munafuka to da kwarankwatsa sae dae a fitar da gawarki dakin nan " Ta Duka da niyar cakumo K'arama amma ta nemeta ta rasa…… Ihu ta k'wala yayin da fitsari ya samu damar sulaluwa ……

  K'arama ta gani tana yawo saman dak'in dauke da katuwar wuka jawur da ita tana cakama iska !Duk lokacin da ta caka wukar Azabar a cikin Kundum take karewa ……Ihu ta farayi tare da zawo tana neman taimako amma babu mai jinta duk mutanen dake cikin gidan ……Yawan K'arama ya linko sau shiddah yayin da manyan hakora suka fito ta karkashin habarta ta fara zagaye Kundum dake fitar da nishi sama sama ……Azabar tsoro ta saka Kundum sandarewa a gurin yayin da ta sulale ta gaba ta fadi saman tarin kasar dake zube a tsakiyar dakinta ……

  Malan Lado kam tunda ya rufe idonshi yana hawaye bai sake budewa ba har sae da tarin matan dake tsakar gidan suka watse sannan Maitafasa ta matso ta zauna kusa dashi tana Fad'in "Ladona Ladona ashe bayan kana kwance Hafsuwalle Bokaye ta fara nema don ka amsa Wannan Mayyar diyarka ce"

  Girgiza kai yayi cike da takaici yana da tabbacin Sharri ne irin na Maitafasa ……

  "Ladona shi yasa naga wannan yarinyar tana zuwa baka abinci ashe magani suke barbada maka a ciki" Ta karashe maganar cikin sigar kwantar da murya……

  Har lokacin bai bude idonshi ba sae dae hawayen dake zuba ……Dariya tayi tace"Yanzu da bakinka Ladona babu sauran kuka yanzu ma jira nake Hansai ta dawo garin don jiya Mai unguwa yace man yau da mairaice zata dawo shi yasa kaga yau ko tafasa banje debowa ba na tanadi gororina da sanduna na dukan Hansai !kai Lado har dae likafanin Hansae na tanada don wallahi karamin yaki zaayi a wannan kauyen yau……Ina Sonka Ladona duk wanda yace zaya tabaka a garimnan to wallahi baya da riba a rayuwa……"

  Shiru yayi ba tare da ya bude idonshi ba haka ta kare zamanta tare da surutun ta bai tanka mata ba ……
    Wani Yaro ya shigo da gudun tsiya yana fadin "Hansai ta dawo Maitafasa……"

 《》《》《》《》

   INA AMARYA SUMAYYA?

    Dakyar Ma'aruf ya shigeta lokacin ba ita kadae ba shi kanshi ya wahala……Azaba da rad'ad'i suka dirar mata lokaci guda yayin da numfashinta ya janye gaba daya ……Ma'aruf kam bai san wainar da ake toya wa ba kawae aiki yake ba tare da ya lura da bata numfashi ba !Tun yanayi abun yana gamsar dashi har ya koma yanayi don dole saboda ya k'asa hakura ya barta !Sae wajen asubah sannan yayi kokarin tilasta kanshi ta hanyar sulalewa kasan rug din dakin ya zube ba tare da yasan inda kanshi yake ba ……

  Sanyin asubah ya hura Sumayya ta ja numfashi da kyar ta kwalla Kara saboda axabar rad'ad'in dake ratsata……Uban gayyar kam Uban tsoki ya saki wanda shi kanshi ya rasa na menene lokaci guda ya dafe cikinshi yana juyi a hankali ……

  Kusan Awa daya tana kuka da karfi tare da kwala mashi kira ta kasa koda motsi !Da kyar ya mike yana kallonta da idanunshi da sukayi jawur lokaci guda ya dauke kai tare da mikewa yana dafa bango ya nufi toilet……

   Ya dade cikin bathtub din sannan ya fito har lokacin yana jin Kukan da Sumayyar take !Tausayinta yaji lokacin da ya fito yaga yarda bedsheet din yayi kaca kaca da jini ……Sae da ya zura kayanshi yayi sallah sannan ya kalleta tayi lamo jikin pillow kukan ya daina fitowa ! Shi kam duk da baya neman mata amma yana zargin akwae abunda Sumayya tayi amfani dashi da ya kusa halaka su haka ……Kit din da Maryam ta saka mashi a mota ya fita ya dauko ya bude ya fito mata da jallabiya baka da hijab ya aje saman gado ya kalleta cikin kulawa yace ta saka ya kaita asibiti……

  Kuka ta saki cikin shagwaba tace "Ka Saka man Ya Ma'aruf wallahi bana iya koda d'aga hannuna……"

  Gyad'a mata kai yayi ya janyota ya cire blanket din da ta rufe jikinta dashi ya fara canza mata kaya !Bala'in da take ji bai hanata tuna Matarnan mai kayan mata tace mata bayan komae ya kammala ta sake saka wani magani dake cikin karamar roba cikin ruwan zafi ta zauna zata sake komawa kamar budurwa……

  Girgiza kai tayi da ta tuno azabar da tasha jiya yayin da wani bangare na zuciyarta ke bata shawarar ta sake gwada may be don farkone shi yasa ta wahala haka ……Kallonshi tayi a sanyaye tace "Ya Ma'aruf ina son zan shiga toilet nayi wanka tukun ……"





*HAJJA CE 👈*
&
*FEEDOHM💞*
[5:56AM, 12/14/2017] 💧💧 Feedohm💞: 💧💧 *ABUNDA KE BOY'E……*
        《Almost True Life Story》

                   🍁🍁
                      💧

© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


        *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*
   *&*
*_K.A.S Precious HAJJA CE👈_*

*SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《Ummana》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
 *Da dukkan masu suna HAFSAT dake duniyarmu*


      Page *45-46*


Ba tare da ya kalleta ba yace "Zamu je asibiti Sumayya……"

  "Wankan na da amfani……" ta fada tana kallon erection dinshi
    Kallonta yayi sannan ya kalli inda hankalinta yake ya saki Dan karamin tsaki ya mike yana zabga mata wani uban kallo ya nufi Bakin gadon ya dauki wayarshi ya kunna sannan ya zo ya sabeta ya fita da ita ……

  Sae da suka je asibitin sannan ta gane kuranta don ba karamin aiki ya mata ba !Sae da aka mata Propofol injection sannan aka mata dinkin ……Doctor din kam bai samu fuskar wa Ma'aruf din dogon sharhi ba ……

  Sae kusan 12 sannan suka dawo gida ya iske Madre ta aiko masu da breakfast mai rai da lafiya !Sae da ya bata taci sae shagwaba take mashi sannan ya bata magungunan da suka basu tayi bacci !tsayawa yayi yana kallonta ba laifi itama ta had'u kuma yana mata son da yakewa yan uwanshi sae dae sam baiyi tunanin zai iya rayuwar aure da ita ba saboda masifar rawan kanta!

  《》《》《》《》《》


  Su K'arama na isa gida suka iske mutanen gidan cirko cirko tsakar gida ummansu kuwa na tsakiya durkushe daga mai dunguri sae mai zagi ……Kallo Da K'arama ta mata ta dauke kai ta koma bakin Bukkarsu ta zauna ta zauna tana duba kafarta inda Maitafasa taji mata ciwo……

  Zulai ta juyo tana kallon Lauratu da tayi mutuwar tsaye tana kuka ganin kaskancin da akewa Ummansu tace "Kuka yanzu kuka fara Lauratu indae har Uwarku bata daina halin bera ba……"

  A Razane take kallon Zulai sannan ta kalli Inno dake tsaye bakin bukkarta tare da kallon Sallau ta sake kuka tana fad'in "Wallahi Ummana bata halin Bera sallau……"

  Gyada mata kai yayi shima kamar yayi kukan yace "Na gasgata Lauratu!Inna Zulai dan girman Allah ku daina abunda kuke yi ku tausayawa wannan baiwar Allah ku bar zuciyarta ta huta!

  Gaba daya suka rafka salati wanda dama sarar mutanen gidan ce yayin da jummai tace "Sallau kaima an jike ka kenan……"

    "Wallahi baa jikeni ba !Shin me ta maku da zaku sakata tsakiya kuna wulakantata haka Inna Zulai?Shin ita ba diyar nan gidan bace ?koko ance maku Inno bata kaunar yarta take zuba maku ido tana kallonku shin ku baku san Kawaici bane inna Zulai……"

  Matar Bedo tace "Yanzu dae Sallau kana kare surukarka !Hafsuwallw daga ido ki kalli Sallau ki ce bake kika Saci Kwanon Man Shanun Inna Zulai ba……?

  Saurin Kallon K'arama sukayi shi da Lauratu sannan ya mayar da kallonshi ga Hafsuwalle dake duke tana hawaye amma ta kasa dagowa ta kallesu ! Tana da tabbacin dakinta aka ga kwanon man shanun amma tayi imani sae dae idan K'arama ta dauko shi……

  K'arama tayi tsallen kura ta dira gaban Umman tata tana dangyasa kafa tare da yarfe hannu baya tace "Abun Sata na Sata ne Zulai……"
  Hafsuwalle ta janyota ta zaunar da ita kasa tana kallonta da rinannun idanunta alamar tayi shiru ……
  Makale Kafada tayi tace "Ba zanyi shirun ba Umma bayan itama man Shanun na sata ne gidan Fulani ta shiga ta iske sun gama kad'i Habee ta shiga daki ta dauko kwarya ta satoshi……"

  Uban Mari Zulai ta zabga mata tana fadin "Dan Ubanki ni zakiwa Sharri K'arama ?In je in sawo man shanun hayin dan malan ki ce sato shi nayi !To da kwarankwasa bara Ardo ya shigo yau sae dae ni ko ku a gidannan ……"

  Mikewa tayi tana Murd'a hannu ta fita yayin da zulai ta cigaba da zabga ruwan tijara yan gidan na tayata !Hafsuwalle da Lauratu kam sun yarda da abunda K'arama ta fad'a sae dae babu wanda ya motsa daga inda yake ……

  K'arama kam gidan Fulani ta nufa ta iskeshi Zaune yana gyara lalataccen kekenshi ……Da yake tasan basu zama inuwa daya dashi don haka ta tsaya daga nesa ra d'aga murya tace "Fulani an kama barauniyar Man shanunku……!
  Da Sauri ya mike ya dauki katuwar sandarshi yana fadin "Ke K'arama ban san shegantaka yasin na iso nan sae na k'wadeki……"

  Tab'e baki tayi tana d'age kafa guda tace "Yasin da gaske nake Fulani Zulai Matar Ardo ce ta sace maku man shanu kuma kazo gidan yanzu na,nuna maku……"

  Kamar sakarai ya biyota har cikin gidan yana fadin "Yasin idan karya kike sae na k'wad'eki……"

  Murgud'a baki tayi tace "Idan da gaske nake fa?

  Washe baki yayi yace "Zan baki naira Goma……"
Dariya tayi sannan suka karasa cikin gidan kallo ya koma kan fulani da K'arama ta shige bukkarsu ta fito da Kwaryar Man shanun da ta kai ta mike mashi tana fadin "Zulai ta Sata shine nima na dauke na kai Bukkar Ummanmu mu dinga sha !Sae suka gani suka ce Ummana ta sata ……"Ta kalli Lauratu tace "Dan Allah yaya Lauratu ba kowa ya rasa ba kenan ?

  Ita kanta Lauratun bata san sadda murmushi ya subuce mata ba ta kama hannun Ummanta ta dagata ta kaita har bakin bukkarsu sannan tace "Allah zaya warware komae Ummanmu……"Daga haka ta juya ganin K'arama ta rike kwarya tana fadin "Bani kudina Fulani sannan kaje ka turo matarka tawa Zulai yarda tawa Ummanmu……" Kudinta ya bata ya juya yana kwafa ……

  Matan gidan kam surutai suka fara yi Kasa kasa sannan suka watse suka bar Zulai da ta fara Borin karya!!!!!

  【】

  Maitafasa kam jin cewa Hansai ta dawo ya sata kwasawa bukkarta da gudu ta dauko wata katuwar gora tare da farin yadi ta fita gidan ! Kirjin Malan Lado ya fara dagawa da karfi saboda masifar bakin cikin dake cike da zuciyarshi ……Lokaci guda numfashinshi ya fara sarkewa hakoranshi suka fara,haduwa da juna !A Hankali ya fara maimaita kalmatusshahada sannan idonshi ya rufe ruf da guntun hawayen da ya gangaro……

   Inda ake aje Mankara Mai tafasa ta leka tare da cilla farin yadin tana fadin "Likafaninki da mankararki Hansai sun shirya "Sannan ta fada gidan Mai unguwar !Cikin Sa'a ta iske Hansai tayi goho tana damawa Shanu dussar ai kowa ta daddage ta maka mata sandar a baya……Kara ta kwalla tare da gantsarewa ta kife cikin dussar don ba karamin duka Maitafasa ta mata ba……

   Matan gidan suka nufo su dakyar suka rirrike Maitafasa da ta cigaba da kwadawa Hansai Sandar bayan ta kaita kasa ……Dakyar suka kwaci Sandar lokacin Hansai an jigatu jini ya wanke mata fuska hannunwanta kuma da take kare dukan sunyi sumtum dasu……
  "Ku barni na Kashe kafura tun kafin ta kashe man Ladona……"Mai tafasa ta fada tare da rarumar katun dutsi ta jefawa Hansai dake jan Kafa ta fada,bukkar Mai unguwa tana kwala mashi kira……

  Da yake matan gidan sun san abunda ke tsakanin Hansae da Maitafasa masu bata hakuri nayi masu turata nayi……
   Hawa take kamar fulawa ta cigaba da fadin "Wallahi ni da ke Hansai Allah kadae ya isa ya shiga tsakani don ko mijinki bai isa ba wallahi !Duniyar nan duk mai shirin kashe man Lado ta wallahi ni zan fara kashe shedani !Ni Uwar Mai tafasa Uwar Lado da ka taba Ladona kara ka kona mai unguwa da ranshi wallahi!

  Da Kyar suka samu ta bar gidan ta fita tana fadin "Wallahi sae na dawo kuma daga yau duk abunda ya samu Ladona sae na dawo na juyeshi a kanki banza bakar munafuka !Yo dake Hansai ba kara Kundum ba faran munafuka akanki baka…Banda jaraba har yanzu baki bar kishi ba dani bayan mijin yayi shekara sha biyar da rasuwa Hansai !Kiyi kishi da Buwale da Kande mana tunda yanzu mijinsu kike aure………"
   Da Haka har ta bar gidan ta shiga gidansu Lanto ta karbo Curin hura uku da nonon Goma ta nufo gida zata damawa Lado……

    Tana shiga gidan ta wuceshi ta dauko kwarya da koshiya ta fito ta zauna tana fadin "Su Ladona bacci aka samu ?
    Shirun da taji ne ya sata cigaba da damun furarta tana yar waka tare da daga murya tace "Wae Kundum lahiya kike shiru?Kundum dake zube tsakar daki bata san me ake ba ……

  Sae da ta gama damun Furar sannan ta matsa tana bubbuga shi tace "Ladona tashi ka kurbi fura sae ka cigaba da baccinka ko?

  Zaro idanu tayi ta wuntsilo ta dawo gefen da yake kallo ganin babu numfashi a tare dashi ta kanga kunnenta a hancinshi tana kiran sunanshi a rude tare da jijjigashi ……

  Kururuwa ta saki tare da dafe Kai tana kiran "Ladona" sannan tayi hanyar dakin Kundum tana kururuwar daya dawo da Kumdum daga duniyar doguwar sumarta……
    A Tare suka fito dakin ko wace ta kama hanyar gabanta ……

  Cikin lokaci Kadan gari ya gauraye da Rasuwar Malan lado yayin da Maitafasa ke kuka kamar zatayi hauka ! Duk wanda yaji rasuwar sae ya tausayawa Maitafasa saboda an san irin son da takewa Lado ……

  Likafanin da ta tanada don Hansai dashi aka nannade Ladonta !Maitafasa bata rage kukan da take ba sae da aka dawo rufo lado Limamin ya kirata yana fada mata cewa a kabarin Lado sun iske ruwa mai sanyi a kwance tare da goro fari kyal guda biyu a ciki ! Sannan ta sassauta kukan da take ……Gida ya cika da mutane har da wasu yan garuruwan amma Kauyen su Hafsuwalle basu san wainar da ake toyawa ba ……



*HAJJA CE 👈*
&
*FEEDOHM💞*
[4:35AM, 12/15/2017] 💧💧 Feedohm💞: 💧💧 *ABUNDA KE BOY'E……*
        《Almost True Life Story》

                   🍁🍁
                      💧

© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


        *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*
   *&*
*_K.A.S Precious HAJJA CE👈_*

*SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《Ummana》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
 *Da dukkan masu suna HAFSAT dake duniyarmu*


       Page *47-48*


K'arama na bisa iccen mangoro Ard'o yazo wucewa Kallonta yayi ya kuma kallonta ganin ta kwantar da kanta jikin wani reshe tana kuka !har zai wuceta yaji ta bashi tausayi karo na farko tun tasowarta don yana da tabbacin bai tab'a gani K'arama a haka ba ……
   Sae da yayi Jim sannan yace "Hafsatu……"
  Kallonshi tayi ta rufe idonta kwallar dake ciki ya gangaro saman kuncinta ……

  Tausayinta yaji sossae ya saka hannu ya daukota ya dire ta k'asa yana tambayarta abunda aka mata ……

  Kasa magana tayi sae dae Hannunta da ta watsa alamum oho……
   Cikin kulawa yace "Wani ya dakeki ne Hafsatu?
  A Hankali tace "Kai ni Bansani ba Ard'o……"

 Gyada kai kawae yayi ya wuceta ya shiga gida !har zaya wuce ta gaban Bukkar Hafsuwallen sae ya kasa !wani bangaren na zuciyarshi na kwad'aita mashi ganin Hafsuwallenshi yayin da Tausayi da Kaunar da yake mata ya tsaya mashi a zuciya !A Sanyaye ya tsaya daga bakin Kofar ya kira sunanta "Hafsatu……"

,,Da Sauri ta fito don tabbatar da ko Ard'on ne ke kiranta kowa gizo muryashi take mata ……Ganinshi ya sata zubewa gabanshi tana goge hawayen farin cikin da suka zubo mata ……

  Kau da Kai yayi yace "Hafsatu ya na ga Hafsatu K'arama cikin damuwa shin ko wani abu ke faruwa ne ?

  Girgiza kai tayi tace "Babu Abunda ke faruwa Ard'o" muryarta na rawa……

   Kallonta yake cike da tausayi tayi bak'i ta jeme kamar ba diyarshi ba !anya ya mata adalci a matsayinshi na Uba?Cikin tausayi yace "Ki je ki daukota Hafsatu Idan yunwa take ji ki shiga cikin bukkata ki dauko fura ki bata na yarje maki Hafsatu……"
 
   Kallonshi take ya dawo mata Ard'onta mai kaunarta……Ta Girgiza kai tana share hawaye tare da murmushi lokaci guda tana kallonshi har ya nufi Bukkar Zulai……Sanan ta mike ta dauko mayafinta ta fita neman K'arama……

     Bakin iccen ta ganta jingine tana dafe da kanta kiranta tayi amma bata amsa ba haka bata dago ta kalleta ba ……Har sae da ta zo kusa da ita ta dafa bayanta sannan ta kalleta tare da fashewa da wani irin kuka !

  "Me aka maki K'arama?Ta fada a hankali tana kallon jikinta da ke kyarma ……
 
    "Baffa Ummana !ance baran sake ganinshi ba "ta fada tare da rungumeta……
 
  Cikin sauri tace "Waya fada maki K'arama?

   Kai tsaye tace "Yar Kudundub'a ce !
Girgiza kai tayi duk da gabanta dake fad'uwa tace "Wacece Yar kudundub'a? Karya take maki Ko jiya ba kinga Baffan naki ba?

  Shiru K'arama tayi tana kallon Umman kafin ta jata da karfin kamar ba ita ba ta nufi Hanyar garinsu Lado!Duk Yarda Umnan taso ta ki zuwa amma ta kasa !har sae da suka isa bakin garin sannan gabanta ya tsananta fad'uwa!Hango mutane a kofar gidan ya tabbatar mata da zancen K'arama……Yayin da taja ta turje bakin wani katon icce tana kuka mara sauti ……

   K'arama na ganin ta tsaya ta saki hannunta ta nufi cikin gidan har lokacin hawaye ke kwance a fuskarta !Kusa da Maitafasa ta rab'a ta zauna tana kallonta Kamar yarda maitafasar ta tsareta da ido tana jan majina ……

  Hannun K'arama Maitafasa ta kamo sannan ta mike ta tsaye ta fashe da kuka tana fadin "Indae ba Hansae ba to Wannan yarinyar ta Kama Ladona"

   Maganganu mutanen dake cikin gidan suka fara k'asa k'asa kafin Kundum dake ta cije lebe tana son tayi magana amma tana tsoron Abunda ya faru ya sake faruwa!daurewa tayi tace "K'arama ko shegiy……"Maganar ta makale yayin da ta hadiye miyan tsoro tana murje idanu……

  Kukan Maitafasa ya tsananta tace "Dan Allah Hafsatu K'arama indae har kinsan ke kika cinye man Lado ki taimaka ki fad'a man a tonoshi ki tsallakeshi ya tashi !wallahi ina son Ladona kamar raina ki taimaka man yar nan na tuba ki yafe man ……" jan majina tayi sannan ta kara da cewa "Ni Maitafasa ban tab'a ganin munafuka mai son raba uwa da d'a ba irin……"ta kuma yin shiru tana kallon K'aramar sannan tace "Na Tuba Hafsatu……"

  Girgiza kai K'arama tayi ta rungume Maitafasa da sauri yayin da Maitafasar ta fara kokarin tureta amma taki Sakita sae Uban kukan da takeyi……


《》 《》《》《》

  Ma'aruf kam yana kokarin bawa Sumayya hakkinta soyayya yake nuna mata dae dae gwargado dan ma wani lokacin rawar kanta na bata mashi rai !Ga Uwa uba rashin sirri duk wanda ya shigo gidan sae ta bashi labarin rayuwar da suke ……Yau ma kamar kullun ya shigo gidan ya iske Beebah kawarta zaune suna fira a falo ……

  Shigowarshi bata sanya Sumayya daina fadin "Ke wallahi Beeba Aure dadi gareshi !ke ni fa yanzu bana kwana bisa pillow sae dae bisa kirjin mijina ……Kin san me yafi birgeni a jikin Ya Ma'aruf?

   Beeba ta girgiza kai yayin da kirjinta ke dukan uku uku don tunda take bata tab'a ganin Ma'aruf ba sae a hoto sae kuma yau !don ko da akayi bikin Sumayya bata kasar sae dae friends dinsu dake ba da labarin kyawunshi……

  Yar Dariya Sumayyar tayi sanna ta mike ta nufi Ma'aruf din tana fadin "Wallahi kawata gashin da ke kwance a kirjinshi shi yafi birgeni sae sajenshi ……Ke bari dae in dawo akwae chapter……" Amsar jikkar dake hannunshi tayi ya mika mata fuska a daure ba tare da ya kalli Kawarta ba

  Kissi ta kai mashi a check dinshi sannan ta rugumeshi tana fad'in "I've Missed your warmety "Sake daure fuska yayi ya wuceta ……Itakam Beeba binshi tayi da kallo har suka rufo kofa sannan ta saki ajiyar zuciya tare da waro yan mitsi mitsin idanunta waje kafin ta dauki wayar Sumayya dake aje bisa hannun kujera tana dubawa ……

   Suna Shiga daki ya watsa mata harara yana cire Coat dinshi !Murmushi tayi sannan ta bude fridge din dake cikin d'akin ta dauko hollandia ta zuba mashi a cup tana fad'in "Welcome Oga……"

  Karba yayi ya kurba tare da zama saman kujera yana fadin "Me ke damunki ne Sumayya?

Bisa cinyarshi ta zauna tana fadin "Me nayi kuma Ya Ma'aruf"

Sae da lumshe ido sannan yace "Kin cika surutu Sumayya mara amfani sannan baki da sirrin mijinki Sumayya!menene na fad'awa K'awa irin wad'an nan maganganun?

  Zunburo baki tayi tace "Laifine don na yaba k'yawun mijina a gaban kawata?

  Girgiza kai yayi hadi da tabe baki yace "A'a ki cigaba"
Shiru tayi tana kissing wuyanshi !ya tureta a hankali yace "am Hungry……!

  Nan da nan ta b'ata Fuska tana fad'in "Ai Laifin Madre ne sae da nace ta samo mana mai aiki amma shiru har yanzu bata samo ba kuma yau ko Lunch ba aiko mana dashi ba……Sae dae mu ci Cake da coke"

  Wani wawan kallo ya watsa mata yace "Ke meye amfaninki "

  Tayi Fari da idanu tace "Na Kula da Kai na tarairayeka kadae !idan an gama abinci nayi feeding dinka da hannuna……"
 
 Tab'e Baki yayi yace "Amma ke bara ki iya dafawa ba?

  Shiru tayi tana turo baki sannan tace "Amma Ya Ma'aruf na maka kama da matan dake girki dan Allah?

   Girgiza mata kai yayi ya mike ya dauki Keys dinshi ya fita har lokacin Beeba na zaune inda suka barta tana ganinshi ta mike tana gyara siket dinta tace "Barka da fitowa Sir"

  Kallo daya ya mata ya kauda kai ya fita tare da daga mata hannu dai dai lokacin Sumayya ta fito tana fadin "Sorry Beeba na barki ke kad'ae wallahi rikeni yayi wae dole sae yaji dumin jikina !Kinsan Ya Ma'aruf da soyayya kawae sae ya fara kissing dina…… yanzu ma da kyar na samu ya barni don sae da nace Ina Son ice cream sannan ya fita ya sawo man wallahi Beeba ya iya tattalin mace……"

  Watsa mata harara Beeba tayi tana fad'in "Ke kau kinji dadinki kawata !Bara nazo na wuce gida !

  Cikin Sauri Sumayya tace "A'a dan Allah ki bari ya dawo ki dauki course yarda ake bawa Amarya abinci ……"ta karashe maganar tana dariya kasa kasa

  Uwar Harara Beeba ta sake mata ta k'asan ido tana yatsina fuska sannan ta fizgi handbag d'inta tayi gaba tana fad'in "Ina da aikin yi Baby ……"















*HAJJA CE👈*
&
*FEEDOHM💞*
[6:52PM, 12/18/2017] 💧💧 Feedohm💞: 💧💧 *ABUNDA KE BOY'E……*
        《Almost True Life Story》

                   🍁🍁
                      💧

© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


        *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*
   *&*
*_K.A.S Precious HAJJA CE👈_*

*SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《Ummana》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
 *Da dukkan masu suna HAFSAT dake duniyarmu*


_Wannan shafin nakune kyauta domin jin dad'in ku, hak'ika *hajjafeedohm* na alfahari daku grps d'in *Feedohm Novell's💞 & Hajja ce 👈novels grp* we so much love you people d'in dake ciki...._😘😅


     Page *51-52*

*T*sawa Ard'o ya daka musu baki d'aya suka yi shiru,inno ma ta k'araso jikinta duk a sanyaye,lauratu kuwa kasa fitowa tayi sai faman kuka take cikin masifa Maitafasa ta kali Ard'o tana mai masifa.

"Kaji dallah can gafara kasa anyi shiru kayiwa mutane tsaye, inzaka yi magana Ard'o kayi kuma kasa mutanan nan su fito komu mushiga ta k'arfi ardun Allah." Mai-tafasa ta fad'i tana yi kamar zata makewa Ard'o fuska, nan da nan mutanen wajan suka suma hayani guru ya kuma kaurewa da maganganu da habaice-habaice.

Cikin bukar kuwa danbe ake sha tsakanin Umma da k'arama, cikin wani mugun kallo da k'arama kewa Ummanta ta kalleta tana huci numfashin ta tamkar ta tattaro ma al'umar garin ta had'a tace wa Umman ta "baza ki kyaleni bane?... *!* tallahin Allah aradu zan makeki na fita wallahi sai na rama dukan da akai miki, Umma ki rabu dani ki kyaleni ki kyaleni." Kalaman da k'arama keta gayawa Umman ta amma ta matseta sai faman naushin cikin ta take yi Umma na kuka sabida azabar zafin da takeji a cikin.

"Ya isa haka kowa yazo ya fita, kubar min yarinya ta ni yanzu na yadda cewar k'arama 'yar lado ce dan...." Ai basu bari ya k'arasa ba suka fara mai tufin Allah tsine inno sai sharar kwallah take domin cin zarafin yayi yawa Mai-tafasa tace, "Aradun Allah Ard'o yau ko kaine Mai-unguwa kace ka yadda k'arama jikar kace sai inda Allah ya barmu bare k'arama mayya ce tacinye min lado lokacin da nake murnar ladona ya warke, yau kama sai k'arama ta bakunci lahira..."

Nufar d'akin suka yi baki d'aya mutanan gurin, kafin kace me sun fito da Umma dake makure da k'arama a jikinta idanun Hafsatuwalle sunyi luhu-luhu sunyi jawur sabida azabar kuka da tashi amma na k'arama a suye sai wani kallon jummai take tana zaro manyan idanuwanta kafin ta tuntsire da dariya tamkar mahaukaciya sabuwar kamu tace "Ard'o kaga inna jummai yau da farau-farau d'in Tanimu tayi karin kumallo ana bashi ta karbe mai idan nayi karya ta bari a bud'e cikin agani..."

'Lahh kaji min shegiyar yarinya nima cinyeni take son yi dama tun data farka yau take kawo min hari Ashe dana fita karfi ne taje tacinye lado shine bata koshi ba take son had'awa dani yanzu na Shiga uku ni jummai Maman Gaddafi..." Mutane suka yi kan k'arama Ard'o da inno suka yi saurin karewa yayin da Umma ke durkushe a gurin ta rik'e cikinta da hannuta lokacin lauratu ta fito bayan ta gano shigowar sallau.....,


*《》 《》《》《》*

"Madre wallahi ni yanzu ban iya yin komai babyn nan yana wahalar dani amma Yaya Ma'ar yayi ta cewa bana kaza bana kaza, kuma nace ki samo min me aiki Madre kinki ni yanzu ya zanyi.. *!* gashi kasala ta kuma yi min yawa." Sumayya ta fad'a tana daga jikin Madre dake rik'e da mediceted glass d'in ta, cikin kulawa da nuna tattali Madre tace.

"Sorry Sumayya na fara bin cika miki, wadda aka samu d'in tana son yi amma 'yata na kwance ba lafiya amma nasa a kuma binciko miki wata me aikin nima ai at this stage zanso ki samu mai temaka miki da wasu abubuwan." Cikin sauri Sumayya ta kalli Madre tare da cewa.

"Yauwa Madre na! Toh yaushe za'a samo? Dan Summay yanzu bata aikin uban komai hatta wanke pant vest, da bra duk ta dena. Madre tayj murmushi tare da fad'in.

"Sai randa aka samu amma nace karya wuce cikin week d'in nan." Lokacin Ma'aruf ya shigo cikin gayun shi, wankan suit yayi white color yayi bala'in yin kyau ya k'arasa ciki tare da gaishe da Madre dake kallon shi cikin mamaki.

"Ma'aruf ina zuwa kuma haka...?!"

Sai daya sauke numfashi sannan ba tare da ya kalli inda suke ba yace "zan je na gano mutumin nan, ina son na tabbatar da ya samu komai hatta sana'ar da zai iya yana daga zaune so flate d'in 2:00pm zan bi." Ya fad'a tare da juyawa zai fita Madre na mishi addu'ar dawowa ita kuma Summaya tayi saurin bin bayanshi. A k'afar fita suka had'a ta matseshi ta baya tare da kissing d'in wuyan shi cikin shauk'i dan ba k'aramin kyau yayi mata ba har wani masifaffan kishi da sha'awar shi suka dirar mata at once.

"Sweetheart please kaje dani." Ta fad'a tana shafar wuyan shi, kallon mamaki yayi mata tare da kallon cikin jikin ta, a zuciyar shi addu'a yake Allah yasa kar babyn shi ya kwaso d'abi'un ta a fili kuma ya janyeta a jikin shi tare da shafar gefen fuskarta yace.

"Bye take care."

Da sauri ya shiga mota driver yaja suka fita yana jimamin halayyan sumayya da be san haka take ba sai bayan sunyi aure.

Yana sauka garin katsina aka had'a shi da guide sai focal person d'in shi suka nufi gwadabniya kauyan su malan lado, tun da suka fara dosar kauyan basu ga mutun ko d'aya ba hakan ya bawa Ma'aruf mamaki sai yaji duk babu dad'i yau ba'a biyo suba har suka je k'ofar gidan. Focal person d'in ya shiga cikin gidan amma tsit hakan yasa shi nufar d'akin da yasan lado na kwance amma shima ba kowa hakan ta dawo ya sanarwa da Ma'aruf,  "what did you said? Toh ina suka tafi baki d'ayan garin? Oh my God... *!*." Ma'aruf ya furta cikin mamaki.

"Mu k'arasa fadar Mai-unguwa wata kila mu asamu bayani." Cewar focal person d'in yana kallon Ma'aruf dake ta faman shafar kyakyawan quarter million d'in fuskar shi "ok." Ya fad'a tare da shiga cikin motar suka wuce kauyan su Hafsatuwalle mamaki fal zuciyar shi.
*《》 《》《》《》*

Da sauri ya k'arasa gurin ta yana tambayar "lauratuna lafiya kuwa? Kama hannuta yayi suka k'arasa gurin mutanan ko wanne da makami a hannunshi can ya hangi Mai-tafasa ga inno da Ard'o suna kare k'arama da Ummanta shima ya k'arasa gurin yana bada hakuri duk da cewar besan meke faruwa ba.

"Wallahi yau sai k'arama ta bi lado ba zasu sake kwana cikin gidan nan ba." Mai-tafasa ta fad'a tana kuka tamkar an mareta yayin da su jummai ma ke ta fad'a cikin karayar muyar inno tace.

"Kuyi hakuri indai k'arama ce da Hafsatuwalle zasu bar muku garin amma karku d'auki mataki akan kashe k'arama...."

"Su tashi subar gidan toh kafin mu kaddamar musu." Ard'o ya kalli inno yaga sai kuka take lallai yau yazama dole su Hafsatuwallen shi su bar garin idan ba haka ba aiyi musu aika aika ya juya yaga Umma sunkuye lauratu ta rik'o ta sai kuka suke yayin da k'arama ke zaune tana kwakular kasar gurin. A gaba suka tasa su mutane jingim Umma ta rik'e da k'arama sai tirjewa take yi akan sai ta saketa taje ta rama dukan da Mai-tafasa tayiwa Umma lauratu sai kuka take ganin ana  korar su da jifa da zage-zage har suka baro gidan suka nufi hanyar barin garin.

Jibgegiyar motar data doso ce ta sa suka tsaya tare da bin motar da kallo, gaban su ta karaso focal person yayi saurin mod'ewa Ma'aruf kofar ya fito cikin nutsuwa tare da karewa mutanan gurin kallo ciki harda Mai-unguwa da shima ya k'araso gurin ba jimawa, wani banzan kallo yake aikawa da Mai-ungawa wadda yasa shi muzurai da idanuwa...........,













*FEEDOHM*💞
&
*HAJJA CE*👈
[10:32PM, 12/18/2017] 💧💧 Feedohm💞: 💧💧 *ABUNDA KE BOY'E……*
        《Almost True Life Story》

                   🍁🍁
                      💧

© *HASKE WRITER'S ASSO*
_Home of expert & perfect writer's_


        *_NA_*
  *_FEEDOHM💞_*
   *&*
*_K.A.S Precious HAJJA CE👈_*

*SADAUKARWA……*
*HAFSAT* 《Ummana》
*HAFSAT* 《Miss Xoxo》
 *Da dukkan masu suna HAFSAT dake duniyarmu*


       Page *53-54*



Kusa da Hafsuwalle ya k'arasa ganin jini a fuskarta a hankali ya tambayeta "Me ke faruwa anan?……Saboda ya lura ita kadae ke da sauran hankali a gurin ……

  Sunkuyar da kai tayi ba tare da tace komae ba sae kukan dake fita a hankali mai cin rai!Mai ungua ya k'araso kusa dashi yana fad'in "Ranka ya dade wallahi yanzu na k'araso na tarad da wannan hargitsin……"

  Kallo d'aya ya mashi ya watsar ya kuma tambayar Hafsuwalle me ke faruwa……K'arama ta ba shi amsa da "Wasan jifa suke da mutuwa shine Maitafasa ta jefe Ummana……"tare da saka hannu a aljihunshi ta fito da katuwar wayarshi da ta lek'o……

  Maitafasa tace "Bani guri buwalle na karashe shegen wasan jifan da tace anayi akan shedaniyar yarinyar can……!

  Wani sakaran kallo ya watsa! kafin yayi magana Mai'ungua ya ce "Yallabai rigima suke akan wannan yarinyar da kake gani!Da farkon fari yarinyar Shegiyace!Sannan Mayya ce!A Kakkabe a kare d'azu ta lashe kurwar Ubanta mutumin nan Malan Lado da ku ka san da zamanshi a fad'in kauyennan……"

  Dafe kanshi yayi yana maimata Inna lillahi wa inna ilahir raju'un!Idan ya fahimci maganar Mai ungua Malan lado ya rasu kenan!Mai tafasa ta katse mashi hanzari ta hanyar watsa mashi tafin hannunta a saman fuskarshi tana fad'in " Bani guri Bature !Ni maitafasa bana daukar iskanci aradun Allah!Kai din wofi baka isa ka hanani daukar mataki ba!Da k'warank'watsa Tunda har ta lashe man Lado to kai din banza baka isa ka hanani kasheta ……"

  Wawan Marin da ya zuba mata ya katse sauran Maganarta !Yayin da tayi baya ta hantsila ta fad'a jikin Kundum……Ji kake Tumm Kundum ta janye jikinta cikin mugunta tana cije baki……

  A fusace ya kalli Mai ungua yace "Ku iskeni gidan Hakimi yanzu!Sannan ya karbi wayarshi dake hannu K'arama ya kalli Hafsuwalle yace "Shiga mu je……"

  Babu Musu ta ja hannu K'arama guard ta bud'e mata motar suka shiga da kyar aka tada motar……

Inno kam Juyawa tayi gurin Ard'o cikin kuka tace "Ka gaza a matsayinka na maihafin Hafsatu Ard'o!ka gaza gurin kula da hakkin da ya rataya a wuyanka,shin kana da wani abu da zaka fad'awa ubangijin da ya baka Hafsatu na banzatar da rayuwarta da kayi? ko kana tunanin Allah bara ya tambayeka akan digon hawayen Hafsuwalle bane!Baka yarda da tarbiyyar diyarka bace ?ko ko Hafsatu ba jininka bace da ka wofintar da ita a idon duniya!Duk abunda ya samu Hafsuwalle ka raba biyu ka dauki kaso daya Ard'o kaine sila da ka kasa warware komae……!A  Hankali ta juya ta kama hannun Lauratu suka shige gida……Ard'o kam tsaye yayi ya kasa koda motsi……

  Kallo d'aya zaka ma Mai'ungua ka gane yana cikin rud'u a sukwane ya kalli Mai tafasa yace "Shi kenan kun janyo mana bala'i Maitafasa!Aradun Allah kafin kice komae a gaban Hakimi sae kinsha tsumagiyar dukan da kikayi masu…"

Cikin sauri tace "Ni kam na yafe Ladona!Mai ungua kaje kace masu suyi hakuri wallahi na tuba!Ni shegiya inje gaban hakimi inci ubana……"

  Kundum ta taba hannu tana fad'in"A A Maitafasa ke da kike neman kudin zuwa birni k'arar Hafsuwalle! Yau kuma kin samu dama ki ce bara ki je ba……"

  Kukan kura tayi ta cakumi Kundum tana fad'in"Na Dade da sanin ke bakar munafuka ce dama Kundum!Gidan Uban wa nace maki ina son kai hafsuwalle birni k'ara?

 Kundum ma cakumar Maitafasa tayi suka kaure da nusar cikin juna yayin da yan garin ke fad'in"Gaskia Kundum ke ce baki da gaskia Yarda Maitafasa ta shiga wannan bala'in kuma ki kawo mata wata maganar……"

  Sakin Kundum din tayi ta watsawa mai maganar harara tace "Dalla gafara munafukai!Ba har daku aka dakesu ba……"

  "Da k'warank'watsa babu ruwana……"Cewar Bulawale yayin da ta tafi buguzum buguzum ta nufi hanyar komawa kauyensu ……Kafin kyaftawar ido matan garin duk sun sab'e an bar Maitafasa da Ard'o sae Mai unguwa dake tsaye kamar sakarae……

   Sae da Mai'ungua yawa Maitafasa jan Ido sannan ta yarda suka hawo mashin d'aya suka nufi birni yayin da Ard'o ya samu mai mashin shima ya bisu……

  Gidan Hakimi suka nufa acan suka iske Hafsuwalle da K'arama zaune cikin fada ……

  Guri suka samu suka rakub'e kafin Hakimi ya shigo!Maitafasa ta rarrafa kusa da hafsuwalle tace "Hafsuwalle baki ji kunyar zama shari'a da ni Maitafasa ba?Haba Hafsuwalle tuno lokacin da kike Amaryar Ladona!Ni ce Zabbi!Ni ce Fura!Ni ce manshanu!Haba Hafsuwalle mu sasanta tun kafin naji tsumagiya a gadon bayana……"

  Karaf K'arama tace"Idan ta tuna lokacin da kika kwala mata k'ota fa……"

  Kafin tayi Magana Hakimi ya shigo tare da Ma'aruf suka zauna dae dae lokacin da Ard'o shima ya shigo ya zube ya kwashi gaisuwa sannan ya kuma ya rakub'e a bango!Maitafasa kam banda mazurai da soshe soshen karya babu abunda take !

 Mai ungua aka nema yayi bayani !Da kyar ya bayar da labarin tun daga farkon rikicin har karshe sae kame kame yake shima yanayi Maifasa na fad'in "Wutarka daban dake Mai unguwa" "Yaushe nace K'arama ta cinye Lado……?ko kuma tace" Allah ya had'a Munafuki da warin kabari……"

  Sae da dogari ya kwatsa mata tsawa sannan ta kama bakinta……

   Hakimi ya tambayi "Wanene Uban Marigayin?
 Mai unguwa yace "Mahaifinshi ya rasu sae dae nine matsayin Ubanshi ranka ya dad'e……"

  Hakimi ya kallesu d'aya bayan d'aya yace"Wacece Uwar marigayin?

   Zumbur Maitafasa ta mike tana fad'in "Gani anan Ranka ya dade!Matsowa zanyi ne koko kai zaka matso yarda zaka ganeni……"Mai ungua ya janyota ta zauna ……

 Hakimi yace "Ina Mahaifin Hafsatu?

Ard'o ya kalli Hakimin sae dae bakinshi ya masa nauyin amsa sunan Mahaifinta!Shi Hafsuwallen ta kalla hawaye na zuba a idonta ta nunashi da hannu……

A Hankali yace "Nine Mahaifinta kafin na zubar da k'imata saboda zancen mutane……"

  Tambayar Maitafasa akayi ko gaskia Mai ungua ya fad'a amma ta karyata rabi da kwatar zancenshi !illa iyaka ta yarda da cewa K'arama ba jikarta ba ce !

 Hafsuwalle kam iyakar gaskiyarta ta fad'a cewa K'arama diyar Ladoce !Shi kanshi Hakimin baya da hujjar da zai karbi zancen Hafsuwallen ko na Maitafasa……

   Ma'aruf kam shiru yayi yana jin dramarsu yayin da yake Kallan K'arama dake harkan gabanta har da su dariya!Sae da taji Maitafasa na fad'in "Da kwarankwatsa ta fad'o mata yanzu bata ce K'arama ta cinye lado ba……"

  Sannan ta kwasa da gudu ta fad'a gidan Hakimin tana fad'in "Aiko zata fad'o maki yanzu……"

  A Cikin gidan ne ta kalli cikin matar Hakimi ta kece da dariya tana fad'in "Yan birni harda ganyen ciyawa suke ci……"

 Daga farkon Matar Hakimin banza ta mata Sae da K'aramar ya janyo hannunta tana fad'in"Baku da tuwo ne kika ci ganye da wake?

  Harara ta watsa mata don ta saba ganin y'an kauye irin haka……Ita kam K'arama binta tayi har kitchen tana fad'in"Jiya kinci Nama da Ankaha yau kuma kinci Ganye da wake shin baku da tuwone ku?Ga yan cikinki duk sun harde guri guda……!

  Matar Hakimi ta kwala ihu yayin da dogari ya shigo da sauri ta fad'a mashi abunda ya faru ya kuwa kama K'arama da kyar ya maidata fada ya fad'awa Hakimi abunda tace ……

  Nanne Maitafasa ta rafka gud'a tace "Ahayye yanzu kam na amsa Nace Mayya ce tunda har tayi ma Matarka……"ta karashe maganar tare da watsa Hannu……

  Hakimi cewa yayi shirman yara ne a kyaleta amma Maitafasa tayi karab tace "K'arama meye a Cikin Hakimi……"

  Cikin rashin Damuwa ta kalli tukeken cikinshi tace " Ni dae wake na gani da wani abu kamar tuwo amma ba tuwo bane……!Aikam Hakimi ya fara mazurai tare da kare cikinshi da hannu ……

  K'arama ta kalli Maitafasa ta kwashe dariya harda tab'a hannu tace"Ke kam Maitafasa banda Tafasa da Zawo a gefe babu abunda nagani……!

  Dariya Ma'aruf ya sake mai sauti ganin abun yake kamar shirme sae da juyo tace mashi "Kaine kad'ae kasha Madarar shanu!

   Kafe ta da ido yayi !Hakimi kam cewa yayi a kira sarkin Mayu yanzu !Cikin mintina kadan Sarkin Mayu ya iso akace ya dubata ko Mayya ce……Duk binciken da yayi ya tabbatar masu da babu Maita illa iyaka Aljanu suka bude mata ido!

Cikin Hikima Hakimi ya neme ya masu sasanci su koma gida sanna yayi wa Ard'o magana akan banzatar da ita da yayi ya nuna masu koda ace K'arama ba diya Lado bace bai kamata su mata haka ba balle Hafsuwalle da auren sannan tsakanin Miji da mata sae Allah!Kuma yanzu babu wanda ya isa ya warware wannan matsalar sae Ubangiji su tafi Allah zai fito da *ABUNDA KE B'OYE* Sannan Maganar K'arama Mayyace bata taso ba tunda ance Aljanune shi yayi alkawari zai sama mata magani har ta warke ……Maganar sakin da Maitafasa tayi wa Hafsuwalle bata taso ba tunda ba Lado ya saketa ba !ta koma gida tayi wa mijinta ta kaba……

  Maitafasa kam datsewa tayi ta fara yayyafa ruwan tijara wae karyane kawae ana so arufe maganar ne ita kam ta rigaya ta saki Hafsuwalle kuma bata da gadon Ladonta!K'arama mayya ce kuma yanzu ta ce ita ta cinye mata Lado babu wasu aljanu don haka dole a bi mata Hakkinta!Sam ta manta gaban Hakimi take yayin da take watsa hannu tana mayarwa tare da girgiza kai……

  Sae da Hakimi yace a mata bulala Goma sannan tayi shiru tana zare ido !Tana ganin za'a daketa ta tuno da lokacin da akayi k'arar Dan gidan Mati a kauyensu gurin mai unguwa……Yaron ya dage yawa Mai unguwa dukan tsiya akace aljanune……Don haka ta saki duwawu ta fara banka Tusa da harba kafafu tana d'aga hannu sama……



*HAJJA CE*👈
&
*FEEDOHM💞*